Adamsy Adam

Adamsy Adam 👨🏻‍❤️‍👨🏻Marubucin Littattafan Luwaɗi Adamsy Adam. Yana kawo muku kayatattun Litattafan manema jinsi a Harshen Hausa.

Litattafan s**an ilimantar su nishadantar su faɗakar, muna fatan zamu kasance tare daku ba tare da cin zarafi A Comment ba 👨🏻‍❤️‍👨

KAZAMIN NAMIJI  10 EpisodKundin Masoya Littafi na (Ɗaya)Rubutawar Adamsy Adam ©️★★★To. Haka na cigaba da zuwa school , A...
09/25/2025

KAZAMIN NAMIJI 10 Episod
Kundin Masoya

Littafi na (Ɗaya)

Rubutawar Adamsy Adam ©️

★★★

To. Haka na cigaba da zuwa school , Abokina Idris da muka hadu tun Ranar da na Fara zuwa shine Abokina Kuma ajinmu Daya wajan Zaman mu Daya.

Kullum tare ake Ganin mu, haka kuma idan Aka tashi zuwa Daukar mu kusan tare ake Tafiya damu,

idris wani Abokinsa Mai Suna Tahir ke zuwa da Adaidaita sahu Yana Tafiya dashi idan an Tashi a School, Ni kuma Yaya Areef ke zuwa Dauka ta A makarantar har kowa ya fahimci irin son da Yaya Areef Yake min. Domin idan Yazo Dauka ta baya taɓa zuwa latti. Wani Lokacin ma Sai dai na fito na Tarar
da Yana jirana a Harabar school,

Rayuwa ta Kam ta Chanja. Ala Dole na koyi Tsafta saboda yadda nake Ganin Yara da manya suna zuwa school tas K**ar ka Lashe su. Amma fa na Sha Duka a wajan assembly kafin na Yiwa kaina fada na rage Kazanta.

Musamman Idris ya zaunar Dani ya nunamin illar barin Yunifom da datti.
Domin idan aka K**a Ni Yunifom Dina Yayi datti a assembly Duka zanci. Ko Kuma su korani Gida.

Dole kanwar naki na koyi Tsafta.🤣

A Haka har muka Zana exam inda nazo na 7 Aka sauya Mana aji zuwa aji uku.

Saidai wannan karon ba Wajan zaman mu Daya da Idris ba Amma ajinmu Guda,. Babu Laifi na kasance mutum Mai hazaka da kokarin haddace Daraussa,

★★★

Yaya major kuwa na jima da bude wani shafi a cikin Littafin Rayuwa ta na Ajiye shi na rufe Gam tare da jefar Dashi ,

Babu shakka Yaya major yana Cigaba da bani Mamaki a duk kwanan Duniya,.

Mummunan Dabi'ar sa ta Kwashe kwashen karuwan maza na Cigaba da Faruwa Akan idona, kuma Ban taɓa Yin Gangancin fada ma Yaya Areef irin Rayuwar da nake Gani akan idanuna Yaya major Yana yi ba. Dukda cewa na Sani Sarai Yaya Areef ya San irin Rayuwar da Abokinsa yake. Ni dai Mubeen Haka na cigaba a da saka Ido.

Yaya major baya Shiga harkata b***e wata magana ta fatar Baki ta hada ni da shi, a fahimatar da nayi Masa shine Dan na Daina Kazanta ne Ina kokarin Zama ɗan Gayu Kuma Ɗan makaranta. Musamman da Yaji Labarin cewa ni Mutum ne Mai hazaka, Yaya Areef ya Sha fada min cewa. Yaya major Yana Matukar Sona da Tausayi na. Amma Abun da Baya so shine kazantar da
nake. Wai Yaya major yace idan har na Daina kazanta to Babu ruwansa Dani bazai Dinga Takura min ba. nakan ce ba Gaskiya bane. Babu Wata kazanta da nake da zai Zama Dalilin da yasa zai Nuna min kiyayya Haka, Dan haka Ko da Gaske ne ko ba da Gaske bane nima na
tsane shi fiye da Yadda ya tsane ni, ni a cikin Zuciya ta sunansa bazai chanja ba , na dauke shi a Matsayin Mutum mugu Marar Tausayi. Marar yafiya Wanda duk Abun da aka masa Sai ya Rama. Marar Karɓar duk kaddarar da ta same shi, bugu da Kari na Dauke shi a Matsayin tambaɗaɗɗe Marar class..

★★★

Yau itace Ranar da Bazan taɓa mantawa ba a Tarihin Rayuwa ta, Itace Rana ta Farko da Al'amarin Rayuwa ta ya Fara Faruwa,. Bayan An tashi daga School tare muka jero da Idris. Labarin Rayuwar sa Yake bani. Inda yace shi Mutumin fataskum ne kuma maraya. Iyayensa sun Jima da Rasuwa. Kanin mahaifinsa ne kadai ya rage Wanda
Kuma Yake neman Raywarsa. Yace min
iyayensa kafin su Rasu sun Tara Masa Dukiya Mai Yawan Gaske. Da kanin mahaifinsa ya fahimci Haka sai ya
Fara farautar Rayuwar sa. Nan ya gudo da duk wasu takardun da suke da
Amfani Ya taho Garin Abuja. Yace min ya Hadu da Haladu Wanda suke tare
a Gidan Haya yanzu Haka. Suna Matukar son juna. Abotar su Mai Matukar Amfani ce,. Dalilin Haka Ya Shiga makaranta Kai tsaye domin Nan Gaba ya samu makami mai karfi
wajan kwato Sauran hakkinsa Dake hannun kanin mahaifinsa.

Hakika na Tausaya ma Labarin Idris.
Inda na Masa kallon Namiji mai kananan shakaru Kuma jajritacce,

Na Tausaya Masa. Babu uwa Babu uba Sai mutum Guda ya rage a danginsa, Mai makon ya tallabe shi ya bashi farin ciki Amma shi ke neman Ransa, Muna Tafiya Yana bani Labari Sai na hango
motar Yaya Areef.

Da murmushi nace. "Ga Yaya Areef can ya Zo daukar mu,

Yana murmushi yace. Mubeen Zan so naji Labarin ka, Na Dade da fahimtar Yayanka Yana Matukar sonka.

Nayi murmushi nace. "Idris kenan. Ai Yaya Areef shine Rayuwa ta, shine Mutumin da ya maye Gurbin Uwa da
ubana. Shine Mutumin da ya Zama babban Yaya. Kani. Kaka. Dan uwa. Da Kuma uwa da uba a gare ni, Baffa baba ya Zama jigon Rayuwa ta

Idris yace. "Waye Kuma Baffa baba.?

Murmushi nayi nace Zan baka Labari Nan ba da jimawa ba,

Da murmushi Akan fuskokinmu muka Karasa Gaban motar Yaya Areef. Ya fito da murmushi Akan fuskarsa.

Idris Yayi saurin risinawa da cewa. "Ina wuni Yaya,

Yana murmushi ya Amsa da Lafiya kalau. Sannan Ya zare gilashin Idanunsa ya kalle ni yace. Student ya Akaji da Karatu.?

Da Sauri na fada jikinsa nace. "Yaya Akwai Wahala.

Dariya su Duka s**ayi min har da Idris. Yace, "To ai Kaima wataran zaka koyar da Wasu.

Yaya Areef ya maida hankalinsa Kan Idris Yace, "To kaji Abokin ka ya fada maka Gaskiya,

Da Sauri Yaya Areef ya Bude min murfin motar na Shiga. Na kalli Idris Dake tsaye nace. "Ka shigo mu kaika Gida Mana.

Yaya Areef ma yace. "Shigo mu sauke ka Mana.

Idris yace. "A'a nagode, yanzu Nima Abokina zai Zo ya Dauke ni,

Yaya Areef yace "Ai baka San zai Zo da Wuri ba. Gara dai mu sauke ka ko,

Idris yace "No kuje Kawai. Idan na biku ya dawo Bai same ni ba ai bazai ji Dadi ba.

Cike da son zolayarsa nayi Murmushi nace. "To Abokin Tahir mu Kwana Lafiya. Sai mun hadu gobe,

Ya daga min hannu Yana Dariya tare da cewa "sai goben.

Daga Haka Muka fice daga School
din,

A Lokacin da muka Shiga Harabar gidanmu a Lokacin jikina ya bani Akwai wani Abu Dake Faruwa a cikin Gidan,. Saboda yadda naji Gidan Yayi Shiru Babu hayaniya ko motsin Mutane. Bance da Yaya Areef komai Akan Haka ba har muka Shiga cikin Babban Falo na Farko. Yaya major na Gani tsaye da jaka Guda Biyu ya Rike Yana fadin ai ba Sai ka dauki komai ba Waɗannan sun Isa har mu Dawo. Ina kallo Yaya Areef ya saka kyalle ya share Hawayen dake kokarin zubo Masa. Nan fa jikina ya bani Akwai Matsala. Zuciya ta ta Shiga wasiwasi.

Yaya Areef ya Kamo Hannuna muka fice daga falon. Duk motocin Gidan Babu sai Guda Daya wacce muka Shiga yanzu muka Tafi.

Yaya major ke tuka mu. muna hawa Kan t**i na samu Karfin Zuciyar Tambayar Yaya Areef

"Ina zamu je,?.

Bai kula ni ba Sai Hawayen Dake bin
Kumatunsa Yana kokarin maidasu suna Nuna Masa Bai Isa ba, Na kalli Yaya major dake tuki Sai Naga ya dauki
kyalle shima Yana share kwalla,

Me zanyi idan ba kuka ba. Nan da Nan nima na saki Nawa kukan wiwi. Idan nasu kukan a Zuciya suke yi Ni Bari na fito Da Nawa fili. Dukda cewa ban San me suke ma kukan ba, Nima Sai na bi yarima Asha kiɗa na Shiga Taya su Rerawa...

🖐🏻

Thanks 🙏🏻

KU DAKACE MU 🙅🏻❤️

09/25/2025

YAU FA RANAR ZUMUNTA NE:
Daga wanne gari kake Ganin wannan posting ɗin.?

BANI BANE   Episod 20baƙar ƙaddaraBook 2 Rubutawar Adamsy Adam ©️ᕦ⁠ʕ⁠ ⁠•⁠ᴥ⁠•⁠ʔ⁠ᕤᕦ⁠ʕ⁠ ⁠•⁠ᴥ⁠•⁠ʔ⁠ᕤᕦ⁠ʕ⁠ ⁠•⁠ᴥ⁠•⁠ʔ⁠ᕤIna cikin ...
09/25/2025

BANI BANE Episod 20
baƙar ƙaddara

Book 2

Rubutawar Adamsy Adam ©️

ᕦ⁠ʕ⁠ ⁠•⁠ᴥ⁠•⁠ʔ⁠ᕤᕦ⁠ʕ⁠ ⁠•⁠ᴥ⁠•⁠ʔ⁠ᕤᕦ⁠ʕ⁠ ⁠•⁠ᴥ⁠•⁠ʔ⁠ᕤ

Ina cikin kuka Ina Jan Ruwa A rijiya cikin wani irin Yanayi marar dadi.

Yaya Kabeer Kuma Bai sake cewa komai ba. Ya fice daga gidan zuciyarsa cike da Tausayina Wanda A iya fuska kadai na fahimta. Ummana ta shige Sashinta ta barni A wajan Ina Aiki Ina hawaye. Kunsan Abinka da Wanda Bai Saba Aikin wahala ba. Kafin Ketowar yammaci na gaji tuɓus, Bayana k**ar zai Kage saboda Aikatau.

A wunin Ranar ba wani Abincin kirki naci ba. Umma da kanta ta debar min A murfin kwano na Shiga dakina na zauna naci. Ko sallah Banyi ba, Domin Lokacin da nake Aiki da naje nace umma ta
Bari nayi Sallah idan yaso daga baya nazo na cigaba rufe ni da duka tayi da maganganu masu zafi. tace Kuma sai na gama Mata Aikinta sannan Zanyi sallah.

To sai Gashi Yanzu ne na kammala Aikin Amma bayana Rike saboda aiki.

Dole haka na mike naje na dauro Alwala na Gabatar da sallolina sannan na Dan shingida. Kunsan dama Daren jiya ba wani bacci nayi ba. Dan haka Ina kwanciya bacci ya tafi Dani..

ᕦ⁠ʕ⁠ ⁠•⁠ᴥ⁠•⁠ʔ⁠ᕤᕦ⁠ʕ⁠ ⁠•⁠ᴥ⁠•⁠ʔ⁠ᕤᕦ⁠ʕ⁠ ⁠•⁠ᴥ⁠•⁠ʔ⁠ᕤ

KAFIN ADNAN YA FARKA BARI MU KOMA BAYA WAJAN BIRTHDAY PARTY DIN DA SU MUSLIHU S**A HALLARA

A Lokacin da Adnan ya bar Wajan birthday party din Aka fara shgalin da ya Tara Samari masu girma. Babu shakka shagali ya kayatar fiye da Tunaninka Mai karatu. Domin Bobo boy na gani tare da Muslihu da Okasha Da sadam da Usman harma da wasu gayu guda biyar suna cashewa Cikin wakar Wani mawaki Mai tashe da kwarewa.

Tabbas Anyi ciye-ciye da Shaye-shaye Kuma An Tiki Rawa tare da jijjiga jiki har 11 na dare sannan Aka watse.

Kunsan Abin da ya daure min Kai?

Wato Lokacin da Aka Tashi A birthday party din sai Naga muslihu da Bobo boy suna Tafiya suna dariya harda Tafa hannaye.

Ni kuma Kuma Adamsy Adam Ina ganin haka nayi saurin zuwa kusa dasu Dan naji me suke cewa, Sai naji Bobo Yana cewa. "Aikinka Yana kyau sosai muslihu. Kuma ga dukkan alamu ba za'a samu matsala ba anan gaba.

Muslihu Yace. "Insha Allahu ba za'a samu matsala ba. Domin na tabbata ba zai taɓa kuɓuta daga wannan Tarkon ba har abada.

Bobo Yayi murmushi tare da cewa. "Haka nake so. Kuma haka nake fatan Ya kasance.

Muslihu yace. "To Yanzu dai ya batun cikon Kuɗina. Ka San fa bani kaɗai nayi Aikinnan ba. Na Gayyato Mutane da Yawa sun taimaka min saboda komai Ya tafi daidai ba tare da wata matsala ba.

Bobo Yace. "Na manta fa. Nawa ne ma cikin kuɗin naka.?

Muslihu Yace. "2 miliyan ne, saboda ina son na sallami wasu da nayi Amfani dasu wajan cimma wannan kudirin.

Babo boy Yayi murmushi tare da cewa. "Kar ka damu zanyi kokari na baka miliyan Uku. Na San zasu isa komai. Ni dai bana son Nan gaba A samu matsala.

Muslihu Yace. "Akan kuɗi zan iya komai. Kuma zan tabbatar da cewa na toshe duk wata hanya da zata janyo matsala. Karfa ka manta idan har aka samu matsala Nima ina cikin matsalar dumu-dumu, Saboda haka ka daina ma wani fargaba Abokina.

Bobo boy Yace. "Wallahi muslihu Idan Aka samu matsala A gaba ni da kaina Zan kasheka da hannuna. Babu ruwana da Alakar dake tsakanina da Kai.

Muslihu na jin haka Ya kwashe da dariya.

Thanks 🙏🏻

KU DAKACE MU 🙅🏻❤️

ATTAJIRAI   Episod 20Duniyar MatsafaBook 2Rubutawar Adamsy Adam ©️ᕦ⁠⊙⁠෴⁠⊙⁠ᕤᕦ⁠⊙⁠෴⁠⊙⁠ᕤA EPISOD DIN DA YA GABATA.Daidai Lok...
09/24/2025

ATTAJIRAI Episod 20
Duniyar Matsafa

Book 2

Rubutawar Adamsy Adam ©️

ᕦ⁠⊙⁠෴⁠⊙⁠ᕤᕦ⁠⊙⁠෴⁠⊙⁠ᕤ

A EPISOD DIN DA YA GABATA.

Daidai Lokacin Jafar da Sooraj s**a karaso wajan Niki-niki da kaya A kansu.

Muneer Ya bisu da kallo. Sai Yaji k**ar Ya kamo Jafar Ya rungume saboda tsananin sha'awa da Shauki. Duk da cewa a cikin datti suke. Domin kallo daya zaka musu kasan cewa sun sha tafiya. Ƙafafuwan su k**ar an tono su daga kabari.

Baba kaka Yace. "Sannun ku da zuwa jikokina irin Albarka. Ku taya ni Godiya Alhaji Muneer Ya kawo mana kyautar kayan abinci,

Da mamaki Sooraj Yace. "Gaba daya wannan kayan,?

Baba kaka Yace. "Kwarai ma kuwa. Shi kenan daga Yau zaku huta da Yawon Bara. Domin har aiki ya samar muku a cikin gidan sa.

Cikin sanyin jiki Sooraj Yace. "Mungode. Allah ya saka da alkairi.

Daga haka Ya shiga gida.

Jafar Yace. "Mungode. Allah ya saka.

Zai shiga cikin gida Muneer Ya dakatar dashi ta hanyar ciro wasu manyan kuɗaɗe dauri biyu Ya mika masa.

Hannun Jafar na Rawa ya karɓa ba tare da ya so hakan ba. Saboda idon Baba kaka da Alhaji Umaru Yana kansa.

ᕦ⁠⊙⁠෴⁠⊙⁠ᕤᕦ⁠⊙⁠෴⁠⊙⁠ᕤ

CIGABAN LABARI....

Jafar Yace. "Duk wannan me za'ayi dasu.?

Muneer Yace. "Naka ne da kai da Sooraj. Idan kuna so zaku iya fara zuwa wajan aiki Gobe. Amma wannan baya daga cikin albashin ku. Idan kunzo zamu daidaita akan albashin da za'a biya ku.

Baba kaka Yayi saurin cewa. "Allah ya saka da alkairi.

Jafar Yace. "Mungode.

Da sauri Ya shiga cikin gida.

Baba kaka da Malam Umaru sai da s**a cika Aljihu da kudi sannan s**a yi sallama da Muneer akan washe gari Jafar da Sooraj zasu fara zuwa wajan aiki a gidan Muneer wanda ya bada Adresehin sa Anan take.

Wasu Yaran Unguwa Aka saka s**a kwashi kayan s**a kai gidan baba kaka aka jibge su a tsohon dakin ajiye dabbobi. S**a fito baba kaka Ya sallame su da wasu yan kudi da basu taka kara sun karya ba,

Sai da s**a tabbatar da tafiyar su Muneer da Fawwas sannan s**a kalli juna da Amininsa Malam Umaru.

Baba kaka Yace. "Kaga arziki har gida.

Malam Umaru Ya riƙe baki Yace. "Tabdi. Haka wannan bawan Allah Ya tara kudi Lokaci guda.?

Baba kaka Yace. "Rabu da ikon Ubangiji wanda ke azurta bawa a duk Lokacin da Yaso.

Malam Umaru Yace. "Kaga. bari na tafi gida. Amma zan dawo Anjima da yamma. Tunda kudi sun samu Baga ta zama ba.

Baba kaka Yace. "Haka ne. Sai zuwa yamman idan mun hadu. Sai mu kasafta kayan a duba wanda Ya cancanci a bashi.

Malam Umaru Yace. "Mutanen unguwar nan fa bakin ciki da hassadar su yanzu ne zasu bayyana shi. Saboda haka dole ne mu tsohe kunnuwan mu da idanun mu.

Baba kaka Yace. "Duk hassadar mutum haka zai hakura Ya barmu. Domin duk baƙin Cikin ɗan tsako bai isa Ya karbi ɗan shirwa ba.

Malam Umaru Yace. "Allah Ya kyuta.

A haka s**a yiwa juna sallama Baba kaka Ya shiga cikin gidan sa. Daidai Lokacin Jafar da Sooraj na zaune bisa taburma. Kudin da Muneer Ya basu na zube a gaban su. Sun zuba uban tagumi. Sun kasa furta ko wacce kalma,

Baba kaka Ya shigo Yana dariya tare da binsu da kallo. Yace. "Lafiya kuwa naga duk kunyi Jugum-Jugum?

Babu wanda Yayi magana a cikin su. Hakan Yasa Ya nufi wajan kudin dake gaban su Ya kwashe su tare da cewa. "maimakon naga kuna murna da farin ciki Allah Ya yanke mana wahala,

Sai A Lokacin Sooraj Yace. "Gaskiya baba kaka sai na faɗa maka gaskiya koda ace zaka rufe ni da duka ne.

A fusace baba kaka Ya daga masa hannu Alamun dakatarwa Yace. "Bana bukata dan ubanka. Kuma ka Rufe min baki. Aiki ne a gidan Muneer sai kunyi.

Sooraj Ya share Hawaye Yace. "Kaji tsoron Allah baba kaka.

Baba kaka Yayi saurin cewa. "Idan banji tsoron Allah ba tsron ubanka zanji?. Lalle Sooraj Rashin kunya da Rashin mutuncin ka kullum sake yin gaba Yake. Wato Saboda Yanzu ka zama cikakken saurayi. Har kayi girman da zaka fada min cewa II naji tsoron Allah. To tun kafin a haifi ubanka nake jin tsron Allah.

Sooraj Ya Girgiza kansa Yace. "Tunatarwa akan kowa wajibi ne. Ba sai wanda Ya girme ka ko ka girma ba. Ka tuna cewa amana aka baka mu. Idan kaci amana Allan ba zai Barka ba. Wallahi abin da kake bai k**ata ba. Kuma kai Ya k**ata ace ka fimu sanin haka.

Baba kaka Ya tsaya da Mamaki Yana kallon Sooraj Yace. "To. Ubana. Bari na zauna ka fada min gaskiya saboda ni ban santa ba . Marar kunya fitsararre. Wallahi Sooraj ka kiyaye ne.

Sooraj Ya mike tsaye tare da cewa. "Haba baba kaka. Akan mun kasance jikoki a gare ka sai ka kaskantar damu A wajan mutumin da Ya tara dukiyar Haramun,

Baba kaka Ya sake baki Yana kallon Sooraj da Mamaki. Yace. "Oho. Wato sharri zaka yiwa Mutumin da Yaji Labarin Bala'i ya same ni Yazo ya taimake ni?

Sooraj Yace. "Ni ba sharri nake masa ba. Amma duk unguwar nan waye bai san cewa Muneer ba mutumin Kirki bane. Hatta dukiyar da ya tara ma Iyayen sa basu yarda da ita ba.

Baba kaka Yayi Salati tare da tsarkake Allah Yace. "Kai Sooraj kaji taron haduwar ka da Allah. A gidan ubanwa kaji wannan Labarin kanzon kurgen.?

Sooraj Yace "Baba kaka kaje kayi bincike, Wallahi Kwanakin baya da ya kawo musu kin karɓa s**a yi sai mutanen unguwa Ya raba ma.

Baba kaka Yayi shiru Yana tunani.

Sooraj Ya cigaba da cewa. "Wace Alaka kake dashi tsakanin ka da Muneer da zai dauki makudan kudade da kayan abinci irin wannan ya baka?. Ka tuna fa ba kai kaɗai ne kayi asarar dabbobi ba. Me yasa bai taimaka ma sauran ba sai kai.

Baba kaka Yace. "Ka gama.?

Sooraj Yayi shiru tare da share Hawayen sa.

Baba kaka Yace. "Idan baka gama ba ka cigaba ina jinka. Ko kuma ka Rufe ni da duka.

Baba kaka Ya fashe da kuka tare da cewa. "Nine nayi sanadin zuwan ubanku Duniya. Sannan dani da matata muka haɗu wajan bashi ingantacciyar Rayuwa har Ya girma Ya mallake ku. Shekara da Shekaru Ayuba Yaki Ya sake Aure baya iyayen ku mata sun mutu. A hannuna Ya barku ina kula daku da Wuya da daɗi har kuka kai wannan munzalin, Amma duk hakan bai sa na muku mugunta ba sai Yanzu. ? Inna Lillahi wa'inna ilahirrajiun,

Baba kaka Ya share Hawaye tare da face majina Yace. "Ko kana so ko baka so sai kunje kunyi aiki a gidan Muneer domin neman abin da zamu ci. Sakarai kawai. Baka isa na saka doka ka tsallake ba. Ko Ubanka idan Ya dawo duniya bai isa na zartar da hukunci Akan ku Ya hana ni ba.

Sooraj Yace. "Ni. Wallahi ba zan je ba. Na gwammace na kwashe kayana na bar maka gidan ka. idan Yaso kowa ya huta.

Baba kaka Yace. "To Lalle sai dai ka bar gidan nan. Dan baze Yiwu na zauna ina cibiyar da katon gardi irin ka ba.

Cikin tsananin damuwa Jafar dake zaune Ya mike Ya fada jikin Sooraj Ya saki kuka mai cin Rai.

Yace. "Yaya Sooraj don Allah karka tafi ka barni. Idan ka tafi waye zai soni.? Waye zai tallafawa Rayuwa ta?.

Cikin Sooraj Yace. "Bani da wani zaɓi sai wannan Jafar. Kayi hakuri.

Jafar Yace. "Karka manta ka min Al'kawarin cewa zaka inganta Karatuna da Rayuwa ta a kusa da kai. Idan ka tafi duk wani farin cikina zai ruguje.

Baba kaka Yace. "Kai Jafar. Sake shi.

A hankali Jafar Ya sake shi tare da ja da baya. Baba kaka Ya damko hannun Jafar Ya riƙe tare da cewa. "Idan kaga dama ka wuce bangon duniya bai shafe ni ba. Duk inda kaje zaka dawo. Domin duniya ta fi bagaruwa iya jima.

A fusace baba kaka Yaja hannun Jafar s**a shiga daki. Sooraj Ya zube saman taburma Yana kuka. Yana tunanin Ranar da wannan Rigima ta baba kaka zata kare.

ᕦ⁠⊙⁠෴⁠⊙⁠ᕤᕦ⁠⊙⁠෴⁠⊙⁠ᕤ

ƁANGAREN YAZID

Kwanaki biyu kenan Yazid Yana fama da Lalurar Hauka. Mubeen da Mubarak ne ke cigaba da kula dashi a gidan su Rulwan har na tsawan Kwanaki biyu.

Kwanan su uku a gidan Rulwan sai Mubeen Ya tafi unguwar su Yazid har inda suke zama suyi shaye-shaye. Anan Ya nuna ma Wasu Yara hoton Yazid.

S**a tabbatar da cewa sun san shi kuma sun san gidan su. Har kofar gidan su Yazid Aka kai Mubeen. Amma bai shiga gidan ba Ya dawo ya fada musu cewa Ya gano gidan su Yazid.

Anan Take s**a saka Lokaci akan washe gari zasu dauke shi su tafi dashi zuwa gida tunda a Lokacin Dare Ya fara yi.

Mubarak kuka kawai Yake Rusawa idan Ya kalli Yazid da halin da Yake ciki.

A kullum idan zasu kwanta bacci sai ya tofa masa addu'a. A Kwanakin da s**a yi a gidan su Rulwan al'amarin Yazid sai gaba Yake. Sai s**a fahimci k**ar duk bayan awa daya haukarsa kara yin gaba take.

K**ar ko wanne dare. A daren Ranar da za'a kai Yazid gida babu wanda Ya Runtsa a cikin su. Yazid Ya haukace musu gaba daya. Daga Ya kwanta zai zabura Ya zuba da gudu Yana fadin Ga shugaban nan zai Damke ni.

Kukan kura da karfin gaske Mubeen da Rulwan da Mubarak suke sakawa wajan kamo Yazid su zaunar dashi ko kuma su kwantar amma Yaki zama kuma Yaki kwanciyar.

Kusan a tsaye s**a kwana. Sai kusan Goshin Asuba Sannan haukar ta dakata.

Wannan Ya nuna cewa Akwai wasu baƙaƙen Aljanu da Suke zuwa kusa dashi suna sake furgita shi.

Kafin wayewar gari Yazid Ya sha Tofin addu'a daga wajan baban Rulwan da Mubarak da Mubeen har da shi Rulwan din. Amma Tamkar Fetur suke sake watsa ma haukar tasa.

Ai kuwa da sassafe basu tsaya komai ba s**a fito da Yazid. Har zuwa Lokacin wasu surutai Yake marasa amfani.

A cikin furucin nasa Yana ambatan shugaba da boka. Kuma ba zai Rabu da Mubarak ba inji shi. Sannan Yana fadin cewa baya son dukiyar Mubarak kadai Yake so.

Yadda Yazid Yake Kiran sunan Mubarak A cikin Haukar da Yake ba karamin daga hankalin Mubakar Yake ba. Musamman idan Ya tuna cewa A Sanadinsa Yazid Haukace.

Wannan batu babu kuskure a cikin sa, Saboda girman son da yake masa shi Yasa ya bijirewa umarnin kungiyar su ta Matsafa neman Jinsi har ta kai ga sun haukata shi.

Suna shiga unguwar basu tsaya a ko ina ba sai A kofar gidan su Yazid. S**a fito dashi daga mota k**ar majinyaci s**a shiga har cikin gidan dashi.

Baba Attine dake zaune tana wanki sai ta mike tsaye tare da Rafka Salati tana kiran Malam baban Yazid dake cikin dakin Karatu.

A Gigice Ya fito. Ya isa gaban su Mubarak da s**a dauko Yazid Yana wasu surutai marasa kan gado.

Malam Yace. "Me Ya samu Yazid.

Baba attine Tace. "Inna Lillahi wa'inna ilahirrajiun. Yazid me ya faru da kai.? Bayin Allah su waye ku. A ina kuka dauki mana Yazid a wannan halin.?

Da sauri Malam Yace. "Kawo musu shimfidar taburma su zauna.

A Gigice ta shimfida taburma duk s**a zauna. S**a saka Yazid a tsakiya. Duk s**a Rike shi saboda kar Ya tashi Ya gudu.

Malam Ya kalle su cikin Rashin sani Yace. "Bayin Allah Su waye ku.? Me ya faru da ɗana Yaizd na Ganshi a wannan halin?.

Gaba daya s**a yi zuru-zuru suna kallon malam. S**a kasa amsa masa. Tsoron fada masa gaskiya suke domin basu san a yadda sai fassara al'amarin ba.

Mubarak ne Yayi karfin hali Cikin kuka Yace. "Bamu san abin da ya faru dashi ba. Lafiyar sa kalau muke tare dashi. Kawai sai gani muka yi Ya saka ihu. Daga nan sai Ya fara wasu abubuwa na marasa hankali k**ar yadda kuke gani.

Baba Attine Tace. "Inna Lillahi wa'inna ilahirrajiun. Kuna nufin Yazid Ya Haukace kenan. Wannan wacce irin baƙar Rana ce ta zo gare ni a Yau.

Malam Yace. "Kalu Inna Lillahi wa'inna ilahirrajiun.

Babu wanda Yayi magana a cikin su sai Surtun Yazid dake ta tashi. Sun jima suna jimamin al'amarin tare da sauraron abin da Yazid ke fada a haukar tashi.

Malam Yace. "Waye Mubarak a cikin ku. Tun ɗazu Yake cewa ba zai Rabu da Mubarak ba,

A hankali Mubarak Yace. "Nine Mubarak baba.

Attine Tace. "Ashe kaine mayen da ka k**a min Yaro. Shine zaka dauko Yan uwanka Mayu ku kawo min shi.?

Sai kuwa Attine ta mike zata fara zabga bala'i. Kirjin Mubarak sai bugawa Yake Dan tsoro. Yana fargabar kar ambaton Sunansa da Yazid ke yi ya zame masa masifa a Rayuwa.

Da sauri Mubarak Ya dafe kirjinsa Hawaye na zuba. Yace. "A'a umma. Mu ba mayu bane.

Malam Yace. "Dakata Attine. Ba haka Za'ayi ba. Ya k**ata abi komai a hankali.

Malam Ya kalli su Yace. "Yara. Ina son ku dubi Allah da Manzonsa ku fada min gaskiyar abin da kuka sani game da haukacewar Yazid. Saboda musan ta hanyar da zamu iya bi mu nema masa lafiya.

Mubeen da Mubarak s**a fashe da kuka. Matuƙar suna son Yazid Ya samu Lafiya dole sai sun tona Asirin kansu. Abin Kunyar da suke aikatawa a ɓoye zai bayyana Ya fito fili. Me yasa ƙaddara tazo musu da irin wannan sigar?.

Cikin kuka Mubarak Yace. "Malam zamu fada maka abin dake faruwa. Amma ina son kayi mana alƙawarin cewa ba zaka kore mu daga gaban ka ba. Kuma ba zaka aibata mu ba. Sannan ba zaka kyamaci ɗanka Yazid ba. Kuma ba zaka kore shi daga bukatar kulawar ka ba.

Baba Yace. "Me kuka aikata da tsanani haka da kuke tunanin zan tozarta ku da ɗan da na haifa?.

Mubeen Yace. "Abin dake faruwa Yayi munin da idanu ba zasu iya kallon ka su fada maka ba.

Sai A Lokacin Rulwan Yayi magana Yace. "kayi hakuri baba. ɗanka Muneer Yana da alaka da kungiyar Matsafa ta manema jinsi wacce aka sani da kungiyar malele.

Salati malam Ya kaure dashi tare da ambaton Inna Lillahi wa'inna ilahirrajiun.

Haka baba Attine ma ta Rike kirji tana salati tare da tafa hannaye tana kallon Yazid.

Mubarak Ya gyara zama Ya basu Labarin duk abin da Yazid ya fada musu. Da kuma ƙoƙarin zuwa gidan boka domin nema masa magani. Inda acan ne Lalaurar Hauka ta same shi.

Hakika malam da baba Attine sun girgiza matuka da jin wannan mugun Labarin. Dama sun jima suna zargin Yadda Yazid Ya fara tara arziki k**ar yadda Muneer da Bab***e duk s**a daukaka a Lokaci guda. Ashe wannan mugun aikin ne ya daukaka su.

Gaba daya wajan babu wanda Ya iya furta ko wacce kalma. Musamman ma iyayen Yazid da suke binsa da kallo cikin mamaki da tausayin halin da yake ciki duk da shine Ya janyo ma kansa.

GIDAN BABA KAKA

Washe gari ma haka baba kaka da Sooraj aka Buga Rigima. Daga karshe dai Ya tilasta ma Jafar fara zuwa gidan Muneer aiki. K**ar yadda Sooraj Yayi ikirarin zai bar gidan hakan ce ta faru.

Haka Sooraj Ya kwashe kayansa gaba daya Ya bar gidan.

Baba kaka Yace. "A sauka Lafiya. Aiki kuma a gidan Muneer Jafar sai Yayi.

Jafar Yana kuka da bakin ciki da tashin hankalin tafiyar Sooraj baba kaka Ya tura shi gidan Muneer. Haka Ya tafi Yana kuka.

Yana zuwa kofar gidan Ya buga geat mai gadi Ya bude. Ya kalle shi sama da kasa sannan Yace. "Wa kake nema.?

Jafar Yace. "Aiki nazo yi. Alhaji ne Yace nazo yau.

Mai gadin Ya bude masa kofar Ya shiga. Daidai Lokacin Fawwas da Muneer s**a fito. Da alama kuma fita zasu Yi.

Da sauri Fawwas Ya zare gilashin idanunsa yana bin Jafar da kallon mamaki wanda ke gaidasu.

Kafin Yayi magana sai Yaji Muneer na cewa. "Jafar Ka shiga ciki ka zauna a falo ina dawowa ko,

Jafar Yace. "To.

A hankali Ya nufi cikin gidan. Duk s**a bishi da kallo daga Muneer har Fawwas,

Fawwas Ya juyo Yace. "Waye nake gani k**ar Jafar a cikin gidan nan?

Muneer Yace. "Jafar ne. Akwai matsala ne.?

Fawwas Yace. "Me ya kawo shi gidan nan.?

Muneer Yace. "Aiki yazo min.

Da mamaki Fawwas Yace. "Aikin me zai maka. Duk yawan masu aikin gidan nan.

Muneer Yace. "Kaga. Bana son tambaya. Wuce ka shiga mota mu tafi.

A fusace Fawwas Yace. "Baka amsa min tambaya ta ba. Me Jafar Yazo yi nan.?

Da mamaki Muneer Yace. "What? Ni kake daga ma muurya

Fawwas Yace. "Eh. An daga maka murya. To Wallahi baka isa ba. Babu wani aiki da Jafar zeyi a gidan nan. Okay. Na gano ka. Wato ka dauko shi ne dan ka ajiye shi ka dinga lalata dashi ko?. Ashe zamana da kai zai iya sawa ka munafunce ni. Bayan ka san cewa ina son Jafar tun kafin ka samu matsayi da ɗaukakan da kake tak**a dashi.

Muneer Ya fusata Yace. "Kai Fawwas. A karskehi na kake aiki. Ya k**ata ka dinga sanin abin da harshen ka zai fada a kaina. Wato ka fi son a kyale shi ya dinga fita yawon barace-baracen a t**i ko.

Fawwas Yaja tsaki tare da komawa cikin gidan domin ya kori jafar.

Da sauri Muneer Ya rufa masa baya.

Fawwas na shiga falo Ya tarar da Jafar zaune. A fusace Yace. "Kai. Tashi ka tafi gida. Kar na sake ganinka a cikin gidan nan,

Da sauri Jafar Ya mike. Daidai Lokacin da Muneer Ya shigo Yace. "Koma ka zauna. Karka sake tashi anan idan ba da umarni na ba.

Da sauri Jafar Ya koma Ya zauna.

Daidai Lokacin wani mai aiki Ya fito. Muneer Yace. "Ka ɗauki Jafar ka kaishi ɓangaren ku. Ka bashi abinci kafin na dawo.

Ɗan aikin Yace. "To. Sannan Ya k**a hannun Jafar s**a nufi cikin wani falo.

Muneer Yace. "Fawwas. Kudi suna iya canja kowa da komai. Da kudi na siya alaƙa da Jafar a wajan kakansa. Kuma alaƙar mu ba mai tsawo bace. Ina son ka fada min nawa zan biya ka ,. Ina son ka sayar min da sha'awar Jafar ba soyayya ba. Domin ni bana soyayya mai tsawo da namiji. Kai ka sani. Na dauki namiji k**ar kwallon mangoro ne. Daga na gama tsotse shi zan jefar na canja wani. Har abada na gama dashi sai dai wani sabon mangoro. To haka na dauki namiji. Kai kanka ka sani. A sati Ɗaya ina harka da maza fiye da talatin. Saboda ina da arziki. Babu abin da kudi ba zai iya mallaka min ba.

Fawwas Yace. "Akwai abin da kudi ka ba zasu taɓa mallaka maka ba. Cika burinka akan Sha'awar Jafar. K**ar yadda kace babu soyayyarsa sai dai sha'awa. Ina me Tabbatar maka da baka da kudin da zaka bani saboda na Barka kayi amfani da Jafar.

Muneer Yace. "Idan kuɗi sun kasa a wajan ka. Zanyi amfani da karfin ikon da kudi ya bani a wajan masu bukatar kudin saboda na mallaki Jafar.

Muneer na gama fadin haka Ya shiga motarsa ya zauna. Anan ya bar Fawwas Yana huci Tamkar zaki a dawa.

Thanks 🙏🏻

KU DAKACE MU 🙅🏻❤️

KAZAMIN NAMIJI   9 EpisodKundin Masoya Littafi na (Ɗaya)Rubutawar Adamsy Adam ©️★★★Bacci Ya kwashe ni da Zazzafan Tunani...
09/24/2025

KAZAMIN NAMIJI 9 Episod
Kundin Masoya

Littafi na (Ɗaya)

Rubutawar Adamsy Adam ©️

★★★

Bacci Ya kwashe ni da Zazzafan Tunanin Dabi'u da Mu'amular da Naga Yaya major Yana yi da Gayun da Yake kawowa. Na fahimci Akwai wata Alaqa a Tsakanin su Mai matukar daure Kai da jefa Shakku A Zuciya. Ban Sani ba ko ni kadai na fahimci irin Mu'amular da Yake da Samarin ko Kuma harda Yaya Areef oho.

Nidai Bacci ne Yayi Awun gaba Dani da wannan Tunanin A Zuciya ta. Ban farka ba Sai dab da sallar Azahar. Shi dinma Yaya Areef ne ya dawo daga office ya
tashe ni. Da ya kalle ni Sai yaga K**ar da damuwa A fuskata.

Yace. "My brother Lafiyar ka kuwa.?

A Hankali na kakalo murmushin dole nace. "Lafiya Lau Yaya.

Yace. "To tashi muje Kichin na Taimaka maka mu hada Abun da zamu ci kafin Karfe 4 ta buga Ka Tafi islamiya.

Nace Masa. "To , na Mike jiki ba kwari nabi bayansa.

Muna Shiga Kichin din yace. "Subhanallahi. Ya Naga Kichin din duk Ya Lalace,.

Na Fara Sosa keya Ina cewa. "Yaya... ai... girkin da nake yi ne,.

Yace. "To Amma fisabilillahi Mubeen Dan kana Girki shine ba zaka Gyara ba. Dubi ko wanke-wanke bakayi ba. Ga Tukwanen duk Sunyi Baki. Kalli manja har kasan tais duk ka Bata ko Ina.

Nace. "Yaya Wallahi Ina Gyarawa.

Yace. "Inda kana Gyarawa ai bazan shigo Naga ka Ɓata komai ba. Ko falonnan ma kafin na fita office nake
Gyarawa saboda na San ba Gyarawa za kayi ba,.

Yaja Tsaki tare da ficewa daga Kichin din Ransa A bace

Da Sauri Nima nabi bayansa Ina bashi Hakuri, Ya Zauna Saman Duguwar Kujera, Na Tsaya a Gabansa tare da shagwabe Fuska Ina bashi Hakuri

Yace "Haka kake son ka Zama Likitan?. Ai Likitoci basa son Kazanta domin har
fadakarwa suke Akan illolinta,.

Nace. "Yaya ai na Daina kazanta kullum Sai nayi wanka.

Yace . "Kullum Sai ka Yi wanka Amma baka chanja Kaya. Kalli fa kayan jikin ka k**ar an tono ka daga ƙabari. Ai kayan da na siyo maka ba na kawo maka bane Dan ka Tara su, na kawo maka ne saboda kayi wanka ka Saka. Kana Gani dai Gorin da yayanka major Yake maka kullum,.

Taɓe bakina nayi na Canja hirar cike da
Shagwaba nace. "Nidai ba Yayana bane,. Kai Kaɗai ne yayana,.

Girgiza Kansa Yayi tare da Kamo Hannuna muka koma Kichin din. Da kansa Ya Hada Ruwan kumfa Yayi wanke-wanke ni Kuma Ina daurayewa.

Yana gamawa Yayi moofin Kichin din ya Goge komai ya mayar mazauninsa. Dafadukar Taliya ya girka Mana wacce taji Kifi Sai kamshi take, na Taimaka Masa muka Kai komai falo , Muka
zauna Muna ci.

Yau itace Ranar Farko da na Fara cin girkin Yaya Areef. .

Nayi murmushi nace. "Yaya Ashe ka
iya Girki,.

Murmushi Yayi yace. "ba Dai ka Fara Santi tun Yanzu ba,

nace "to ai Yaya Dole nayi Santi Dan ko wata mace ba zata kaika iya Girki Mai Dadi Haka ba,.

Yace. "To Naji. Yi maza ka cinye kaje kayi wanka ka Tafi islamiya,.

A Hankali na Dan Bata Rai nace. "Yaya nifa na Yi Wanka tun Da safe,.

Yace. "Haka zaka Tafi islamiya din kana tsami?,.

A hankali na fara shinshina jikina Amma banji komai ba. hakan yasa na Shagwaɓe Fuska tare da cewa. "Ni bana tsami,.

Yace. "To ai Kai ba zaka ji Tashin da kake ba Saidai wani Yaji.

Fashewa da Kuka nayi. Domin Yaya Areef Bai Taba fitowa ga da ga ya fada min Haka ba. Mutumin da duk Wanda ya Fadi laifina akan Kazanta suke batawa dashi Shine yau da Kansa Yake jifana da Furucin,.

Nace. "Yaya kaima ka Zama Yaya major Kenan ko. Shiekenan gaba dayanku babu Mai Sona,

Sai na Mike na Nufi hanyar dakina,. Bai Biyo ni ba har Saida ya Gama cin Abincin sa. Ya Shigo Yana murmushi.

Yace. *Haba Yaro daga fada ma Gaskiya Sai kayi fushi,. Kar kaga Ina goyon Bayan ka fa saboda bana Jin Dadin yadda ake maka ne. Amma ni kaina bana son Kazanta. Kalli fa yadda ka bar dakinka a Yamutse.

Sai kuma ya nufi toilet Dina ya bude. Da Sauri ya Rike Hanci tare da cewa. "Innalillahi wa'inna ilaihirrajiuna. Haba Mubeen, kalli toilet Dinka yadda ka mayar dashi. Ga zarni ga wari.Yaushe rabonka da wanke Bathroom dinka,?

Bance komai ba Sai ma Tashi da nayi na Shige bayin hade da Turo kofa. Ina jinshi yana cewa. "taya zaka iya Numfashi har Kayi wanka a Wannan bayin. Gaskiya Dole na kawo Dan Aiki,

Ina Daga cikin bayin nace. "Eh din ka kawo Dan Aikin,

yace. "To na fasa Kawo Dan Aikin Kai zaka Gyara , Kuma kayi maza ka fito ka Tafi islamiya,

Sai ya nufi durowa ya fito da Yunifom din Yana cewa. " La-la. to ai Yunifom din ma Yayi datti.

Ina Daga bayin nace. "To a dinka min sabo Mana.

Murmushi Yayi Yace. "Hmmm.

Daga Nan ban sake Jin Motsinsa ba har na Gama jika jikan wankan na fito , ban damu da Shafa man shafawa ba na zira
Yunifom din Na Dauki Alkurani Mai Girma na fice, ban Ganshi A Falo ba, Dan yanzu Haushin Yaya Areef nake ji Sai na Huce Zan Daina ji, na fice Kai Tsaye. ina saka Kafata a babban
falon fita nayi Ido Biyu da yaya major,.
Wannan karon shi Kaɗai ne a Falon Yana kallon TV, da Alama Yana jiran Labaran Duniya na Karfe 5 na Yamma ne,.

Ganin da Nayi mun hada Ido yasa na Fara kokarin fita da sauri. Saidai taku uku nayi naji ya Kira ni,.

"Kai....

Tsayawa nayi chak k**ar gunki a Wajan. Ban juyo ba Kuma ban Amsa ba,. Ban ankara ba na Ganshi A Gabana. Sai kuwa ya fashe da Dariya tare da Rike Baki Yana Kare min kallo daga sama har Kasa,

Yace. "Kai wane irin kazami ne, kazantacce Abun kyama, wato makarantar islamiyar ma ka Fara nuna
musu halinka na Kazanta,.

Da Sauri na fara Dube dube a jikina. Nan take Na fada kogin Tunani, A iya sanina yanzu yanzu na fito daga Wanka. Kuma Yunifom Dina beyi datti Sosai ba, inda
Yayi datti Sosai ai Yaya Areef bazai barni na fito Dashi ba,.

Ina cikin duba jikina naji wata Murya na Fadin. "Baby na waye wannan Kuma me kake fada Masa?.

A Hankali muka juyo daga ni har shi muka kalle shi,. Wani Sabon gay ne kuma. Wato shi kullum Sabon Namiji Yake kwasowa kenan. To ai samarin dake binsa sune Kazaman. Ga mummunan kazanta Nan a tare dashi Amma Yake aibata ni,

Tunanina ne ya katse Lokacin da Yaya major din yace. "Wallahi Ina Nan, A wajan wani Banza kazami, Wai makaranta zashi a Haka kalli Gaban
Rigarsa,.

Sai a Lokacin na lura da Gaban Rigar Yunifom Dina. Manja ne a jiki duk ya Bata ni. Na tuna Lokacin da hakan ya faru a Kichin Bayan na dawo daga makarantar islamiya naki cire Yunifom din nayi girki dashi a jikina, Nan take naji haushin kaina tare da wata kunya
Mai Tsanani ta Lullube ni,

gay din ni Yake kallo Haka Yaya major ma idonsa na kaina cike da kyama da tsana, da sauri na juya na koma ciki tare da fashewa da Kuka.

Da Yaya Areef nayi Karo. Yace. "Yazu daga bangaranka nake na Duba Daki Naga baka Nan. Amma Me ya faru kake kuka.? Na Shiga ciki ne dan na dauko maka Sabon Yunifom saboda kala Biyu na saka aka dinka maka. Da Sauri na karba ba tare da na faɗa Masa
Abun da ya faru ba.

Na shiga dakina na canja na fito tare da yin Taku Daya Bayan Daya cikin tak**a da Allah ya bani Yaya Areef dina.

Na fice Babban falon Karshe hankalina
kwance. Saidai banji Dadi ba da Naga banga kowa ba , na so ace na hadu da yaya major yaga yadda na sauya Sabon Yunifom, Domin ya Sani cewa Mai uwa A gindin murhu baya cin tuwonsa Gaya.

★★★

Washe Gari Litinin Yaya Areef da kansa ya Shirya Kaini school a Karo na Farko. Na ji Dadi Sosai. S**a bani aji. Domin acewar su na yi Girman da ba za'a Kaini ajin Yara ba. Nan fa aka saka ni a ji Biyu. Sun bani Litattafai da duk wani Abu da Zan bukata.

A Lokacin da yaya Areef ya fito daga ajinmu ya barni ji nake K**ar nayi Kuka. Haka ya tafi ya barni a aji tare da Sauran Yara da nufin Idan an tashi Kar na tafi ko ina yace na Tsaya a Bakin get zai dawo ya Dauke ni,

Haka aka Cigaba da Darasi. Ni dai ban Tsinci ko wanne Darasi da Zan Fahimta ba tunda ba turanci nake ji ba. Haka dai aka tashi yin Hutu. A zatona an tashi
ne Ashe break aka Fito. Har na Yi Haramar Fita daga makarantar Naji wani gay na kwala min Kira.

"Mubeen Areef, Mubeen Areef,

da mamaki na juyo da Tunanin waye Haka ya San Sunana a wanann fadin makarantar,. Tsayawa nayi har sai da ya karaso kusa Dani. Ya bani hannu Muka Gaisa.

Yace. "Ina zaka je Haka.

Murmushi nayi nace. "Zan tafi Waje na Jira yayana yazo ya Dauke ni mu tafi Gida,.

Da mamaki Yace. "Gida Kuma?. Me ya faru.?

Da Murmushi AKan fuskata nace. "Ai an Tashi daga makarantar Sai Kuma Gobe,

Yace. "No ba'a tashi ba an dai fito break ne za'a koma.

Nace "meye Kuma Haka.?

Yace. "Ai an fito a huta ne a ci Abinci Sai a koma ,

Nace. "oho.. ai ban Sani ba.

Yayi murmushi yace. "Muje aji ko.

Muna cikin Tafiya Nace. "Amma ya kayi ka Sanni?

yace. "Baka kula Dani ba. Ai ajinmu Daya Kuma wajan zaman mu Daya. Duk Zaman da mukayi baka Gane ni ba?.

Nace. "Ayya.. ai Ni ba Ruwana da Shiga Harkar mutane Abun da ya Kawo ni shi nake.

Yace. "Hakane , Nidai Sunana Idris Abdulaziz.

Nace. "Nidai sunana Mubeen Dukda Naji ka kirani Dazu.

yace. *okay

Nace "Amma ya kayi kasan Sunana.?

Yayi murmushi yace. "Dazu yayanka Yana fada ma Malamin mu Naji

Hmmm Tare da Idris muka nufi aji muka zauna. Abincin da yaya Areef ya siya min tare muka ci har aka tashi break muka koma aji aka Cigaba da
Darasi. Wannan karon na Dan Fara Fahimta saboda Idris Yana Dan koya min,

Thanks 🙏🏻

KU DAKACE MU 🖐🏻

Address

Iuka, MS

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Adamsy Adam posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category