20/12/2021
atar Adam Zango ta farko maman dansa Haidar ta dawo harkar fim
Post published:December 18, 2021
Reading time:4 mins read

AIKA ZUWA SHAFUKAN SADARWASHARE THIS CONTENT
Opens in a new windowTwitter
Opens in a new windowFacebook
Opens in a new windowGoogle+
Opens in a new windowWhatsApp
Amina Uba Hassan, tsohuwar matar fitaccen jarumin Kannywood, Adam A Zango, ta dawo harkar fim da karfin ta a matsayin babbar jaruma.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Amina wacce aka fi sani da Maman Haidar ta fara fitowa a cikin fina-finan Kannywood a farkon shekarar 2000, daga nan ne kuma ta auri Adam A Zango a shekarar 2007.
Bayan auren su da Adam A Zango, sun samu karuwar da namiji a shekarar 2008, wanda shine babban dan Adam A Zango, inda a lokacin Zango ya yiwa Ali Nuhu takwara ake kiran shi da Haidar. Daga bisani kua auren nasu ya samu tangarda inda s**a rabu.
Jarumar dai ta yi shiru ba a sake jin duriyar ta ba, sai dai a wata hira da tayi da mujallar Weekend Magazine ta kamfanin Daily Trust, bayan fitowar ta a cikin shirin fim din Jaruma, ta amsa tambayoyi game da dawowar ta masana’antar.
A cikin hirar an tambayeta abin da ya ja ra’ayinta ta shiga fim, inda ta bayyana cewa asali ita fim din Hausa ma baya burge ta, sai fina-finan Turawa ne da rawa suke burge ta, inda ta bayyana cewa har wata kungiyar rawa ta shiga, inda daga bisani wata rana aka zo ana daukar wani shirin fim din ‘yan Kaduna kusa da su a Abuja, taje wajen kallo, inda a nan ne ta fara magana da daya daga cikin jaruman, a nan ne abokanan ta s**a bata shawarar ta fara harkar fim tunda tana jin turanci za ta iya yin fim din Nollywood da Kannywood, inda wannan ya zama dalilin da ya sanya ta shiga harkar fim.

Sai dai da aka tambayeta ko har yanzu tana da sha’awar komawa Nollywood ta bayyana cewa tsohon mijinta Adam A Zango ya taba bata shawarar hakan, amma akwai rawar da baza ta iya takawa ba a cikin fina-finan su, haka kuma addini da al’ada ba zai bari tayi ba, amma ta ce ba a san me gobe zata haifa