Kungiyar Hada Kan Matasan Sokoto North da South

Kungiyar Hada Kan Matasan Sokoto North da South kasance daya daga cikin matasan da zasu amfana ta fannoni daban daban kamar enganta elimi rege xaman banxa da janyo hankalin matasa da sudogara dakansu

jagora!!!
10/11/2025

jagora!!!

03/04/2025

Allah ya jikan malam Abdul'aziz Dutsin tanshi, Wanda Allah ya yima rasuwa yanzu

Malam Bashir gidan kanawaShaihin malami ne Kuma yana da tausayi da Kuma taimakon mutane Da wannan muke yabawa da irin ko...
21/02/2025

Malam Bashir gidan kanawa
Shaihin malami ne Kuma yana da tausayi da Kuma taimakon mutane
Da wannan muke yabawa da irin kokarinda yakeyi ba dare ba Rana
Allah ya Kara bashi lafiya da iKon taimakawa Ameen

17/02/2025
'Yan bindiga sama da 100 s**a taru yayin sace Manjo Janar Maharazu Tsiga (Mai ritaya) da wasu mutane a Katsina. Karanta ...
11/02/2025

'Yan bindiga sama da 100 s**a taru yayin sace Manjo Janar Maharazu Tsiga (Mai ritaya) da wasu mutane a Katsina. Karanta abin da mazauna yankin s**a fada a sashen sharhi.
Hoto: ||X

Wani jigo a jam’iyyar APC ta jihar Sokoto, Comrade Faruk A. Shehu, ya bayyana damuwarsa kan yadda ake tafiyar da jam’iyy...
11/02/2025

Wani jigo a jam’iyyar APC ta jihar Sokoto, Comrade Faruk A. Shehu, ya bayyana damuwarsa kan yadda ake tafiyar da jam’iyyar a jihar, yana mai gargadin cewa idan ba a dauki matakin gyara ba, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba zai samu nasara a jihar a zaben 2027 ba.

A cewarsa, jagororin jam’iyyar APC a jihar na nuna rashin kulawa da masu ruwa da tsaki da s**a taka rawar gani wajen samun nasarar Tinubu a zaben 2023, musamman tsohon Sanatan Sokoto ta Kudu, Sanata Ibrahim Abdullahi Danbaba.

Ya ce Sanata Danbaba ne ya fi kowa kokari a jihar wajen ganin nasarar APC, inda ya kashe dukiya mai tarin yawa fiye da sauran jiga-jigan jam’iyyar. Haka kuma ya yi amfani da iliminsa da fasaharsa wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar, amma yanzu ba a ba shi wani matsayi a matakin kasa ko jiha.

A cewarsa, da ya kamata a bashi kujerar Minista amma ba a yi hakan ba, sannan kuma ba a bai wa magoya bayansa wani mukami a jihar ba – babu kwamishina, babu S.A, hatta shugabancin kananan hukumomi ba a ba su ba, duk da cewa Sanata Danbaba ne ya ba da kaso 45% na kuri’un da APC ta samu a 2023.

Comrade Shehu ya yi gargadin cewa idan Sanata Danbaba ya fice daga APC, jam’iyyar ba za ta iya samun nasara a Sokoto ba saboda kusancinsa da talakawan jihar.

Ya bukaci Shugaban APC na kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da ya dauki matakin gaggawa don ceto jam’iyyar a jihar Sokoto, tare da ba da hakki ga Sanata Danbaba domin ya cigaba da hidimtawa al’umma.

A cewarsa, idan ba a dauki mataki ba, magoya bayan Sanata Danbaba za su fito zanga-zanga ta lumana domin nuna rashin amincewa da irin yadda ake tafiyar da jam’iyyar a jihar.

Address

Sokoto

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kungiyar Hada Kan Matasan Sokoto North da South posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share