02/09/2026
BARAZANAR ‘YAN BINDIGA A KEBBE: DAN’IYA YA CE APC TA GAZA WAJEN KARE JAMA’A
Ɗan takarar gwamnan jihar Sokoto na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Hon. Manir Muhammad Dan’iya, ya yi kakkausar s**a kan sabuwar barazanar da ‘yan bindiga s**a yi wa garin Kebbe, inda s**a buƙaci a biya Naira miliyan 40 cikin kwanaki bakwai, tare da barazanar kashe mazauna garin da ƙona gidaje idan ba a cika buƙatarsu ba.
Dan’iya ya ce irin wannan lamari abin kunya ne kuma wata babbar shaida ce cewa matsalar tsaro a Sokoto ta kai matakin da ba za a ƙara ɗaukar ta da wasa ba.
A cikin wata sanarwa da Mai Taimaka masa kan Harkokin Yaɗa Labarai, Aminu Abdullahi, ya fitar, Dan’iya ya ce bai kamata a samu yanayin da ‘yan bindiga za su iya sanya wa al’umma haraji, su tsayar da musu wa’adin biyan kuɗi, sannan su yi barazanar hallaka jama’a ba tare da gwamnati ta ɗauki matakin gaggawa ba. Ya ce rahotannin da ke cewa an bai wa al’ummar Kebbe wa’adin kwanaki biyar kafin daga bisani a tsawaita shi zuwa kwanaki bakwai, bayan roƙon jama’a, ya nuna irin girman matsalar da ake fuskanta.
Dan’iya ya ce gwamnatin APC a Sokoto dole ta amsa wa jama’a tambaya mai sauƙi: Me ta yi a cikin shekaru uku da s**a gabata domin kawo ƙarshen wannan matsalar? Ya tuna da alkawuran da aka yi wa jama’a kafin zaɓen 2023 cewa za a ba da fifiko ga tsaro, yana mai cewa maimakon jama’a su samu kwanciyar hankali, wasu al’ummomi na ci gaba da fuskantar hare-hare, sace-sacen mutane, gudun hijira da kuma tilasta musu biyan kuɗaɗen da ‘yan bindiga s**a sanya.
Ɗan takarar ADC ya ce rashin tsaro ba wai yana jefa rayukan jama’a cikin haɗari kaɗai ba ne, har ma yana lalata noma, kasuwanci, ilimi da tattalin arzikin karkara. Ya soki yadda ake ci gaba da gudanar da harkokin siyasa a lokacin da wasu al’ummomi ke rayuwa cikin fargaba, yana mai cewa babban aikin kowace gwamnati shi ne kare rayuka da dukiyoyin jama’a kafin duk wani abin da ya shafi siyasa ko biki.
Dan’iya ya yi kira ga Gwamna Ahmad Aliyu da gwamnatin tarayya da su ɗauki barazanar Kebbe a matsayin gaggawar tsaro, su tura ƙarin jami’an tsaro da kayan aiki, su ƙarfafa tattara bayanan sirri da sintiri, tare da tabbatar da cewa an kare Kebbe da sauran al’ummomin da ke cikin haɗari kafin wani hari ya faru. Ya kuma buƙaci hukumomin tsaro su yi aiki tare da sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma domin gano hanyoyin da ‘yan bindiga ke amfani da su da kuma dakile shirinsu tun kafin su kai hari.
Hon. Dan’iya ya ce lokaci ya yi da jama’ar Sokoto za su tambayi gwamnati sakamakon alkawuran da aka yi musu, ba wai kawai sabbin alkawura ba. Ya jaddada cewa ADC na neman damar samar da shugabanci da zai mayar da tsaro, kare rayuka da dukiyoyi, farfaɗo da tattalin arzikin karkara da jin daɗin jama’a a matsayin babban abin da gwamnati za ta fi mayar da hankali a kai. “Sokoto ba za ta iya ci gaba da rayuwa cikin tsoro ba. Jama’a suna buƙatar gwamnati da za ta kare su, ta saurare su, kuma ta ɗauki mataki kafin bala’i ya faru—ba gwamnati da za ta jira sai an rasa rayuka sannan ta fara neman mafita.”
Sa Hannu:
Aminu Abdullahi
Mai Taimaka wa Ɗan Takarar Gwamna kan Harkokin Yaɗa Labarai