Office of the Commissioner, Ministry for Religious Affairs, Sokoto State.

  • Home
  • Nigeria
  • Sokoto
  • Office of the Commissioner, Ministry for Religious Affairs, Sokoto State.

Office of the Commissioner, Ministry for Religious Affairs, Sokoto State. This is the official page of the Honourable Commissioner, Ministry for Religious Affairs, Sokoto. This page is run by a student of Sheikh

Follow this page for updates on all ministry activities.

Mai Girma Kwamishinan Harkokin Addini na Jihar Sokoto, Hon. Dr. Jabir Sani Maihula, na taya daukacin al’ummar Jihar Soko...
27/05/2026

Mai Girma Kwamishinan Harkokin Addini na Jihar Sokoto, Hon. Dr. Jabir Sani Maihula, na taya daukacin al’ummar Jihar Sokoto, Najeriya da al’ummar Musulmi na duniya baki ɗaya murnar Babbar Sallah (Eid-el-Kabir).

Yana mai roƙon Allah Madaukakin Sarki da Ya karɓi ibadun da aka gudanar, Ya karɓi aikin hajjin mahajjatanmu tare da dawo da su gida lafiya. Allah Ya ci gaba da wanzar da zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban jiharmu da ƙasarmu baki ɗaya.

Allah Ya maimaita mana cikin ƙoshin lafiya da yalwar arziki.

Rubutawa: Jabir Abubakar Wakili
27/05/2026

24/05/2026

ZIYARAR KWAMISHINAN LAMURAN ADDINI DR. JABIR SANI MAIHULA A MASALLACIN SHEHU DOMIN GANIN YADDA AIKIN KE TAFIYA.

AYI KALLO LAFIYA.

KWAMISHINAN LAMURAN ADDINI YA ZIYARCI AIKIN SABUNTA MASALLACIN SHEHU USMAN ƊAN FODIYOA cigaba da bibiyar muhimman ayyuka...
23/05/2026

KWAMISHINAN LAMURAN ADDINI YA ZIYARCI AIKIN SABUNTA MASALLACIN SHEHU USMAN ƊAN FODIYO

A cigaba da bibiyar muhimman ayyukan ci gaban addini da gwamnatin jihar Sokoto ke gudanarwa, Mai girma Kwamishinan Lamuran Addini na jihar Sokoto, Dr. Jabir Sani Maihula, ya kai ziyarar gani da ido a aikin sabunta Masallacin Sheikh Usmanu Ɗan Fodiyo da ke gudana a jihar.

Aikin sabunta masallacin na gudana ne karkashin jagorancin Mai girma Gwamnan Jihar Sokoto, Dr. Ahmed Aliyu Sokoto, PhD, tare da kulawar Ma’aikatar Lamuran Addini ta Jihar Sokoto, a matsayin wani bangare na kokarin gwamnatin jihar na bunkasa harkokin addini da kyautata wuraren ibada.

Kamar yadda aka sani, fifita lamuran addini da tallafawa harkokin addinin Musulunci na daga cikin muhimman ajandodin gwamnatin Dr. Ahmed Aliyu Sokoto.

Yayin ziyarar, ɗan kwangilar da ke gudanar da aikin ya bayyana cewa aikin ya kai kusan kashi hamsin cikin ɗari (50%) na matakin kammalawa. Ya kuma bayyana cewa jinkirin da aka samu ya samo asali ne daga yadda aka fara aikin tun daga tushe domin tabbatar da inganci da ɗorewar ginin.

Haka kuma, ya tabbatar da cewa sun tanadi dukkanin kayan aikin da ake bukata tun kafin lokaci, abin da ya ce zai taimaka wajen hanzarta aikin da kuma tabbatar da kammala shi cikin kankanin lokaci, in sha Allah.

A nasa jawabin, Dr. Jabir Sani Maihula ya bayyana cewa wannan ita ce ziyara ta uku da yake kaiwa wajen aikin tun bayan fara shi, domin tabbatar da cewa ana gudanar da aikin yadda ya kamata.

Kwamishinan ya yaba da yadda ya tarar ana cigaba da aiki yadda ya dace, tare da jinjinawa ɗan kwangilar kan ƙoƙari da himmar da yake nunawa wajen tabbatar da nasarar aikin.

Haka kuma, ya yi kira gare shi da ya ƙara zage damtse domin ganin an kammala aikin cikin lokacin da aka tsara.

Jabir Abubakar Wakili
Ofishin Kwamishinan Lamuran Addini na Jihar Sokoto

AN KADDAMAR DA SABON GYARAN MASALLACIN JUMU’A NA AMANAWAA cigaba da kokarin gwamnatin Jihar Sokoto na bunkasa harkokin a...
22/05/2026

AN KADDAMAR DA SABON GYARAN MASALLACIN JUMU’A NA AMANAWA

A cigaba da kokarin gwamnatin Jihar Sokoto na bunkasa harkokin addini da gyaran wuraren ibada, a yau an kaddamar da sabon gyaran da aka yi wa Masallacin Jumu’a na Amanawa dake karamar hukumar Dange/Shuni.

Gwamnan Jihar Sokoto, Dr. Ahmed Aliyu, yayin taron ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da aiwatar da ayyukan alheri da cigaba masu anfani ga al’umma, musamman wadanda s**a shafi harkokin addini da kyautata rayuwar jama’a.

Masallacin ya samu kaddamarwa ne daga Hon. Umar Ajiya, dan takarar kujerar Sanatan Sokoto ta Gabas, wanda ya yaba wa gwamnatin jihar bisa irin muhimmancin da take bai wa harkokin addini da gyaran wuraren ibada a fadin jihar.

Kwamishinan Lamuran Addini na Jihar Sokoto, Farfesa Dr. Jabir Sani Maihula, ya bayyana cewa gwamnatin jihar karkashin jagorancin Dr. Ahmed Aliyu na ci gaba da gudanar da ayyukan gyara, sake ginawa da kaddamar da masallatan Jumu’a a fadin jihar domin kara inganta harkokin addini da samar da ingantattun wuraren ibada ga al’umma.

Haka kuma, Kwamishinan ya bayyana cewa jajircewar gwamnatin jihar wajen tallafawa harkokin addini ya sanya yanzu kusan babu ranar Juma’a da za ta wuce ba tare da an bude ko kaddamar da wani sabon masallacin Jumu’a da aka gyara ko sake ginawa ba a fadin jihar.

Bikin kaddamarwar ya samu halartar manyan baki, malamai, shugabannin addini da sauran al’umma daga sassa daban-daban na jihar.

Jabir Abubakar Wakili
Office of the Honourable Commissioner for Religious Affairs
Sokoto State.

22/05/2026

Limamin Masallacin Juma’a na Zunnuraini Usmanu Ɗan Affan dake shiyar Sabon Fegi, yankin Gidan Igwai a Jihar Sokoto, Liman Ahmad Usman Attahiru wanda aka fi sani da Malam Osama, ya yaba da irin tallafin da Gwamna Ahmed Aliyu ke bai wa limamai da malamai musamman na Sallar Layya, a cikin huɗubarsa ta yau.

Haka kuma, Liman Ahmad ya bayyana cewa shi da ladaninsa tare da na’ibinsa sun amfana da wannan tallafi.

Rubutawa: Jabir Abubakar Wakili

A yi kallo lafiya.

21/05/2026

GWAMNA DR. AHMED ALIYU YABA LIMAMAI DA MALAMAI TALLAFIN KUDIN RAGON LAYYA

AYI SAURARO LAFIYA.

MONDAY TUSHEN AIKI!A yau Litinin, Maigirma Kwamishinan Lamuran Addini na Jihar Sokoto, Dr. Jabir Sani Maihula, ya shiga ...
18/05/2026

MONDAY TUSHEN AIKI!

A yau Litinin, Maigirma Kwamishinan Lamuran Addini na Jihar Sokoto, Dr. Jabir Sani Maihula, ya shiga ofishinsa domin ci gaba da gudanar da ayyukansa na yau da kullum.

Bayan gudanar da wasu muhimman ayyuka, Kwamishinan ya gana da jama’a da dama kamar yadda ya saba, inda ya saurari bukatunsu tare da ba da shawarwari da umarnin da s**a dace.

Haka kuma, ya ziyarci ofishin Daraktan Gudanarwa na Ma’aikatar Lamuran Addini domin duba yadda ake ci gaba da aikin tura tallafin Sallar Layya da Gwamnatin Jihar Sokoto ke bayarwa ta karkashin ma’aikatar ga malamai da limamai a fadin jihar.

A yayin ziyarar, Kwamishinan ya yi kira ga Daraktan da sauran masu kula da aikin da su tabbatar an gudanar da aikin yadda ya kamata, tare da tabbatar da cewa dukkan malamai da limamai sun karbi sakonninsu a cikin asusun ajiyarsu.

Labari: Jabir Abubakar Wakili
Litinin, 18/05/2026

17/05/2026

JAWABIN MAIGIRMA KWAMISHINA DR. JABIR SANI MAIHULLA, A WURIN KADDAMARDA LITTAFIN { FAITH FOR LIFE NIGERIA }, WANDA UNICEF TASSHIRYA.

TARON WANDA YAGGUDANA A BABBAN BIRNIN TARAYYA ABUJA.

Address

Sokoto

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Office of the Commissioner, Ministry for Religious Affairs, Sokoto State. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share