16/03/2023
TARON KARSHE NA MATA, NA GANGAMIN YEKUWAR NEMAN ZABEN GWAMNONI TARE DA YAN MAJALISUN JAHA NA ZABEN 2023
A Jiya Laraba ne, Mai girma Gwamnan Jahar Sokoto Hajiya Mariya Aminu Waziri Tambuwal tare da Matar Dan takarar gwamnan jihar Sokoto Karkashin tutar Jam'iyyar PDP Malama Asiya Saidu Umar Ubandoma, hadi da Shuwagabannin Jam'iyyar PDP Mata na jahar Sokoto sun Halarci taron yekuwa na karshe na neman zaben dan takarar gwamnan jahar Sokoto da yan Majalisun jaha wanda ya gudana a women Development center dake kan titin dasuki road, a cikin garin Sokoto Central Senatorial District.
Inda aka yi jawabi na musamman daga mata shuwagabannin Jam’iyar PDP, daga karshe avikin jawabin matar Dan da karat gwamnan jihar sokoto Malama Asiya Tayi Kira ga mata musamman iyaye Akan suyi tunanin goben su da Na diyan su akan shugaban da zasu zaba, Tayi fatan nasara ga Jam’iyar PDP baki daya.
Taron ya samu halatar matar gwamnan jihar sokoto inda ta samu wakilcin Prof. Aisha Madawaki, Matar Dan takarar gwamna,Matan chairman din Jam’iyar PDP, matan sakataren Party, BOT ta kasa ta jam’iyar PDP, matan comishinoni, comishinoni mata, matan Chaimomi, Zonals, DG’s, Ma’aikatan gwamnati na din dindin, SA’s da sauran jiga jigan matan ya Siyasa da mata yansiyasa.
16-03-2023.