11/12/2020
🍀AMFÃNIN TAƘAWA A DUNIYA🍀
2020
✍🏼 Gõdiya ta tabbata ga Allah wanda ya sanya jin tsõronsa ya zamanto mafi alherin guziri inda Allah (SWT) yake cewa:
{{وَتَزَوَّدُوا فَإِنَّ خَيْرَ الزَّادِ التَّقْوَى وَاتَّقُونِ يَا أُولِي الْأَلْبَاب}} البقرة: ١٩٧
📚 Ma’ana:- “…Kuma kuyi guzuri. To, mafi alherin guzuri yin taƙawa. Kuma ku bi Ni da taƙawa, ya ma’abuta hankula.”.
Da kuma faɗinSa Maɗaukakin Sarki:
{{يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اتَّقُوا اللَّهَ حَقَّ تُقَاتِهِ وَلَا تَمُوتُنَّ إِلَّا وَأَنْتُمْ مُسْلِمُون}} آل عمران: ١٠٢
📚 Ma’ana:- “Yã ku waɗanda s**a yi imãni! Ku bi Allah da taƙawa, a kan hakkin binSa da taƙawa, kuma kada ku mutu fãce kuna mãsu sallamawa (Musulmi)”.
👉🏽 Sannan Allah ya haɗa jin tsõronsa “Taƙawa” da kõwane irin aikin da Musulmai za suyi a rãyuwarsu da ibãdarsu da mã mu’ãmalarsu.
👉🏼 MA’ANAR TSÕRON ALLAH (SWT) “TAƘAWA”:
📗 --Taƙawa a Lãrabce: kalma ce da take nufin kãriya ko kuma duk wani abu da mutum zai yi amfãni da shi don ya kãre kansa daga wani abu da yake tsõro.
📗 --Amma a wajen Malaman Musulunci Taƙawa nã nufin mutum ya sanya wani shãmaki ko kãriya tsakaninsa da abin da Allah ya haramta don gujewa azãbar Allah.
👉🏼 --Sayyidna Aliyyu ɗan Abi ɗãlib (R.A) ya fassara jin tsõron Allah “Taƙawa” da cewa:
📚 “Taƙawa ita ce jin tsõron Allah mai Girma da kuma aiki da Alƙur’ãni, sai kuma wadãtar zuci ga duk abin da Allah ya baiwa bãwa, da kuma tãnadi don tafiya ƙiyãma”.
✍🏼 Alƙur’ãni mai girma ya faɗakar game da taƙawa a ãyõyi da dãma, sannan ya ambaci amfãni da fã’idõjin taƙawa a duniya da mã lãhira, gã kaɗan daga cikin amfãnin da taƙawa ke janyõwa bãyi tun a rãyuwar duniya:
👉🏽 1—Taƙawa na janyo al’amuran bãwa suyi sauƙi, ba tãre da shan wahalã ba; kamar yadda Allah (SWT) Ya faɗa:
{{وَمَنْ يَتَّقِ اللَّهَ يَجْعَلْ لَهُ مِنْ أَمْرِهِ يُسْرًا}} الطلاق: ٤
📚 Ma’ana:- “…Kuma wanda ya bi Allah da taƙawa, (Allah) zai sanya masa wani sauƙi daga al’amurinsa”.
👉🏽 2—Taƙawa na sanyã wa bãwa kãriya game da cutar-war shaiɗan; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
{{إِنَّ الَّذِينَ اتَّقَوْا إِذَا مَسَّهُمْ طَائِفٌ مِنَ الشَّيْطَانِ تَذَكَّرُوا فَإِذَا هُمْ مُبْصِرُون}} الأعراف: ٢٠١
📚 Ma’ana:- “Lalle ne waɗanda s**a yi taƙawa idan wani tãshin hankali daga Shaiɗan ya shãfe su, sai su tuna (Allah) sai gã su, sun zama masu basira”.
👉🏽 3—Taƙawa na janyo buɗe albarkatu daga sama da ƙasa; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{وَلَوْ أَنَّ أَهْلَ الْقُرَى آمَنُوا وَاتَّقَوْا لَفَتَحْنَا عَلَيْهِمْ بَرَكَاتٍ مِنَ السَّمَاءِ وَالْأَرْض…}} الأعراف: ٩٦
📚 Ma’ana:- “Kuma dã lalle ne mutãnen alƙaryu sun yi imãni kuma s**a yi taƙawa, dã, haƙiƙa, Mun buɗe albarkõki a kansu daga sama da ƙasa…”.
👉🏽 4—Taƙawa na janyõ wa bãwa dãcewa wajen ban-bance tsakãnin ƙarya da gaskiya; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا إِنْ تَتَّقُوا اللَّهَ يَجْعَلْ لَكُمْ فُرْقَانًا وَيُكَفِّرْ عَنْكُمْ سَيِّئَاتِكُمْ وَيَغْفِرْ لَكُمْ وَاللَّهُ ذُو الْفَضْلِ الْعَظِيم}} الأنفال: ٢٩
📚 Ma’ana:- “Yã ku waɗanda s**a yi imãni ! Idan kun bi Allah da taƙawa, zai sanya muku mararraba (da tsõro) kuma Ya kankare ƙananan zunubanku daga barinku. Kuma Ya gãfarta muku. Kuma Allah ne Ma’abocin falala mai girma”.
👉🏽 5—Taƙawa na fitar da bãwa daga wahala da tsanani, sannan ya sãmu hanyõyin arziƙi ta inda bãwan bai sani ba; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{وَمَنْ يَتَّقِ اللَّهَ يَجْعَلْ لَهُ مَخْرَجًا () وَيَرْزُقْهُ مِنْ حَيْثُ لَا يَحْتَسِب…}} الطلاق: ٢ - ٣
📚 Ma’ana:- “…Kuma wanda ya bi Allah da taƙawa, Allah zai sanya masa mafita (*) Kuma Ya arzuta shi daga inda bã ya zato…”
👉🏽 6—Taƙawa na sanyã wa bãwa dãcewa ga jiɓintar al’amarin Ubangiji, da kuma kasancewa cikin waliyyan Allah; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{…إِنْ أَوْلِيَاؤُهُ إِلَّا الْمُتَّقُونَ وَلَكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لَا يَعْلَمُون}} الأنفال: ٣٤
📚 Ma’ana:- “…Bãbu majiɓintanSa fãce mãsu taƙawa. Kuma mafi yawansu ba su sani ba”.
👉🏽 Da kuma faɗinsa Maɗaukakin Sarki:
📚 {{…وَاللَّهُ وَلِيُّ الْمُتَّقِين}} الجاثية: ١٩
📚 Ma’ana:- “…Kuma Allah ne Majiɓincin mãsu taƙawa”.
👉🏽 7—Taƙawa na zama sababin daina jin tsõro daga mãkircin kãfirai; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{…وَإِنْ تَصْبِرُوا وَتَتَّقُوا لَا يَضُرُّكُمْ كَيْدُهُمْ شَيْئًا إِنَّ اللَّهَ بِمَا يَعْمَلُونَ مُحِيطٌ}} آل عمران: ١٢٠
📚 Ma’ana:- “…Kuma idan kun yi haƙuri kuma kuka yi taƙawa, ƙullinsu bãya cutar ku da kõme. Lalle ne, Allah ga abin da suke aikatãwa Mai kewayewa ne”.
👉🏽 8—Taƙawa na sanya bãwa rashin cutar ƴan uwansa bãyin Allah; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{قَالَتْ إِنِّي أَعُوذُ بِالرَّحْمَنِ مِنْكَ إِنْ كُنْتَ تَقِيًّا () قَالَ إِنَّمَا أَنَا رَسُولُ رَبِّك}} مريم: ١٨ - ١٩
📚 Ma’ana:- “Ta ce, “Lalle ni, ina neman tsari ga Mai rahama daga gare ka, idan ka kasance mai tsõron addini!” () Ya ce, “Abin sani kawai, ni Mnazon Ubangijinki ne…”.
👉🏽 9—Taƙawa na janyo girmama shari’o’in Ubangiji Maɗaukakin Sarki; kamar yadda Allah yake cewa:
📚 {{ذَلِكَ وَمَنْ يُعَظِّمْ شَعَائِرَ اللَّهِ فَإِنَّهَا مِنْ تَقْوَى الْقُلُوب}} الحج: ٣٢
📚 Ma’ana:- “Wancan ne. Kuma wanda ya girmama ibãdõdin Allah, to, lalle ne ita (girmamãwar) tanã daga ayyukan zukãta na ibãda”.
👉🏽 10—Taƙawa na janyõ wa bãwa Allah ya karɓi ayyukansa kyãwãwa, sannan kuma ya yafe masa ayyukansa munãna; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اتَّقُوا اللَّهَ وَقُولُوا قَوْلًا سَدِيدًا () يُصْلِحْ لَكُمْ أَعْمَالَكُمْ وَيَغْفِرْ لَكُمْ ذُنُوبَكُم}} الأحزاب: ٧٠ - ٧٢
📚 Ma’ana:- “Yã ku waɗanda s**a yi imãni! ku bi Allah da taƙawa, kuma ku faɗi magana madaidaiciya () Ya kyautata muku ayyukanku, kuma Ya gãfarta zunubanku…”.
👉🏽 11—Taƙawa na sanya sauƙaƙa murya a inda Manzon Allah (SAW) yake a lõkacin rayuwarsa da ma bãyan wafãtinsa, kai har ma yã yinda ake karanta Hadisansa; kamar yadda Allah (SWT) yake faɗa:
📚 {{إِنَّ الَّذِينَ يَغُضُّونَ أَصْوَاتَهُمْ عِنْدَ رَسُولِ اللَّهِ أُولَئِكَ الَّذِينَ امْتَحَنَ اللَّهُ قُلُوبَهُمْ لِلتَّقْوَى لَهُمْ مَغْفِرَةٌ وَأَجْرٌ عَظِيم}} الحجرات: ٣
📚 Ma’ana:- “Lalle waɗanda ke runtsewar saututtukansu a wurin Manzon Allah, waɗannan ne waɗanda Allah ya jarrabi zukãtansu ga taƙawa. Sunã da wata irin gãfara da ijãra mai girma”.
👉🏽 12—Taƙawa na janyo Allah Ya so bãwansa; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{بَلَى مَنْ أَوْفَى بِعَهْدِهِ وَاتَّقَى فَإِنَّ اللَّهَ يُحِبُّ الْمُتَّقِينَ}} آل عمران: ٧٦
📚 Ma’ana:- “Na’am! Wanda ya cika alkawarinsa, kuma ya yi taƙawa, to, lalle ne Allah Yana son mãsu taƙawa”.
👉🏽 13—Taƙawa na janyõ wa bãwa sãmun ilimi mai albarka; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{…وَاتَّقُوا اللَّهَ وَيُعَلِّمُكُمُ اللَّهُ وَاللَّهُ بِكُلِّ شَيْءٍ عَلِيم}} البقرة: ٢٨٢
📚 Ma’ana:- “…Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma Allah Ya sanar da ku. Kuma Allah ga dukkan kõme Masani ne”.
👉🏽 14—Taƙawa na janyõ wa bãwa sãmun rahamar Ubangiji a duniya da kuma lãhira; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{…وَرَحْمَتِي وَسِعَتْ كُلَّ شَيْءٍ فَسَأَكْتُبُهَا لِلَّذِينَ يَتَّقُونَ وَيُؤْتُونَ الزَّكَاةَ وَالَّذِينَ هُمْ بِآيَاتِنَا يُؤْمِنُون}} الأعراف: ١٥٦
📚 Ma’ana:- “…kuma rahamaTa, ta yalwaci dukkan kõme. Sa’an nan zã Ni rubutã ta ga waɗanda suke yin taƙawa, kuma sunã bãyar da zakka, da waɗanda suke, game da ãyõyinMu muminai ne”.
👉🏽 15—Taƙawa na janyõ wa bãwa rashin tawayar lãdan ayyukansa a duniya da lãhira; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{…إِنَّهُ مَنْ يَتَّقِ وَيَصْبِرْ فَإِنَّ اللَّهَ لَا يُضِيعُ أَجْرَ الْمُحْسِنِين}} يوسف: ٩٠
📚 Ma’ana:- “…Lalle ne, shi wanda ya bi Allah da taƙawa, kuma ya yi haƙuri, to, lalle ne Allah bã Ya tõzarta lãdar mãsu kyautatãwa”.
📚 16—Taƙawa na janyõ wa bãwa sãmun bushãra a nan duniya da kuma lãhira; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{…الَّذِينَ آمَنُوا وَكَانُوا يَتَّقُونَ () لَهُمُ الْبُشْرَى فِي الْحَيَاةِ الدُّنْيَا وَفِي الْآخِرَة}} يونس: ٦٣ - ٦٤
📚 Ma’ana:- “Waɗanda s**a yi imãni kuma s**a kasance sunã yin taƙawa () Sunã da bushãra a cikin rãyuwar duniya da ta Lãhira….”.
👉🏽 17—Taƙawa na janyõ wa bãwa sãmun kyakkyãwar shiriya tagari; kamar yadda Allah (SWT) yake faɗa:
📚 {{الم () ذَلِكَ الْكِتَابُ لَا رَيْبَ فِيهِ هُدًى لِلْمُتَّقِين}} البقرة: ١ - ٢
📚 Ma’ana:- “A. L. M. () Wancan ne Littafi, bãbu shakka a cikinsa, shiriya ne ga mãsu taƙawa”.
📚 18—Taƙawa na sanya bãwa ƙin yin zãlunci yãyin wasiyya a lõkacin mutuwa; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{كُتِبَ عَلَيْكُمْ إِذَا حَضَرَ أَحَدَكُمُ الْمَوْتُ إِنْ تَرَكَ خَيْرًا الْوَصِيَّةُ لِلْوَالِدَيْنِ وَالْأَقْرَبِينَ بِالْمَعْرُوفِ حَقًّا عَلَى الْمُتَّقِين}} البقرة: ١٨٠
📚 Ma’ana:- “Kuma an wajabta, a kanku, idan mutuwa ta halarci ɗayanku, idan ya bar wata dukiya, wasiyya dõmin mahaifa da dangi bisa ga abin da aka sani; wajabce a kan mãsu taƙawa”.
👉🏽 19—Taƙawa na sanya bãwa biyan haƙƙin mãtarsa yãyin da rabuwa ta shiga tsakaninsu; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{وَلِلْمُطَلَّقَاتِ مَتَاعٌ بِالْمَعْرُوفِ حَقًّا عَلَى الْمُتَّقِين}} البقرة: ٢٤١
📚 Ma’ana:- “Kuma waɗanda aka saki suna da dãɗaɗãwa gwargwadon hãli, wajabci a kan mãsu taƙawa”.
👉🏽 20—Taƙawa na janyõ wa bãwa makõma tagari mai dãɗi a ƙiyãma; kamar yadda Allah (SWT) yake cewa:
📚 {{هَذَا ذِكْرٌ وَإِنَّ لِلْمُتَّقِينَ لَحُسْنَ مَآب}} ص: ٤٩
📚 Ma’ana:- “Wannan tunãtarwa ce, kuma lalle mãsu bin Allah da taƙawa, suna da kyakkyãwar makõma”.
👉🏽 Da kuma faɗin Allah (SWT):
📚 {{…فَاصْبِرْ إِنَّ الْعَاقِبَةَ لِلْمُتَّقِين}} هود: ٤٩
📚 Ma’ana:- “…Sai ka yi haƙuri. Lalle ne ãƙiba tanã ga mãsu taƙawa”.
✍🏼 Abba Lawan Hassan {Abu Aysha}
KU YAƊA WANNAN ZUWA 'YAN UWA MUSULMA