26/02/2024
NEMAN TAIMAKO .......
Assalamualaikum warahamatullah,
Zanyi Amfani da wannan dama,Na naiman taimako daga gareku iyayen gidana,
Da kuma 'yan kauswa da 'yan siyasar da s**a saba yiwa addini hudima,Ga wata dama ta Samu na taimakawa addinin Allah ta hanyar sadaqaijjariya .........
Babu shakka duk Wanda yasan makarantar Malam shu'aibu Ahmad madallah"Darul kuranil Karim"yasan cewa makarantar ce da samun irinta awannan yanayi da muke ciki zaiyi wahalar Samu,
SABODA ......
Sabida makarantace da take koyar da addinin islama ta hanyar koyar da karatun Alkur'ani mai girma tare da samin ma"Amin sa,Sannan makarantace da take koyar da Tauhidi da fiqihu da sauran hukunce hukunce da musulinci ya tanadar....
AHALIN YANAZU......
Ahalin yanzu makarantar tana buqatar wadaceccen fili wanda zai dauki dukkan daliban da suke zuwa Maza da Mata,Ahalin da ake ciki a yanzu har takai wasu daga cikin daliban basa samun damar shiga cikin makarantar sabida rashin wadaceccen fili.....
ALHAMDLILLAH.....
Makarantar ta mallaki wani gida dayake kusa da ita wasu daga cikin dalibanta,Wanda ahalin yanzu ana buqatar rushe wannan gida domin qarawa makarantar fadin fili,
Da Ni da Ku wannan aikin mune domin gina wannan makaranta,
Amatsayin ka na wanada yake yawaita yiwa addini hidima,Yanzu ma ga dama ta samu,Zamu kaika har makarantar domin ka gani da idon ka don ka gina makarantar,
IDAN KANA DA HANYA.....
Idan kana da hanyar da zaka kawo mana wanda zai gina wannan makaranta muna buqatar hakan.