08/06/2026
Ba za mu taɓa saurarawa ƴanbindiga ba - Tinubu
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatinsa za ta ƙara ƙaimi wajen rage matsin tattalin arziki da jama’a ke fuskanta, tare da ci gaba da yaƙi da matsalolin tsaro da kuma tabbatar da kuɓutar da mutanen da ke hannun masu garkuwa da mutane.
An bayyana wannan saƙo ne ta bakin Sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, a wajen taron addu’ar haɗin gwiwar majami’u da aka gudanar a Abuja domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya ta 2026.
Akume ya taya ‘yan Najeriya murnar cika shekaru 27 na mulkin dimokuraɗiyya ba tare da katsewa ba tun daga shekarar 1999, yana mai yabawa jaruman gwagwarmayar ranar 12 ga Yuni da s**a sadaukar da rayuwarsu wajen dawo da mulkin dimokuraɗiyya.
Ya amince da cewa matsalolin tsaro, garkuwa da mutane da kuma ƙaura daga muhallai na ci gaba da addabar al’umma, amma ya ce gwamnati tana sane da waɗannan ƙalubale kuma tana ɗaukar matakan magance su.
Dangane da tsaro, ya jaddada cewa kare rayuka da dukiyoyin jama’a na ci gaba da kasancewa babban fifiko ga gwamnatin tarayya, yana mai cewa gwamnati ba za ta miƙa wuya ga ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga ko masu aikata laifuka ba.
Akume ya kuma yi kira ga matasa da su guji shiga harkokin daba, tashin hankali na siyasa, yaɗa ƙarya, ƙiyayyar ƙabila da rashin haƙuri na addini yayin da ake tunkarar zaɓen shekarar 2027.
Ya bukaci shugabannin addinai, sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin farar hula da kafafen yaɗa labarai su ci gaba da inganta zaman lafiya, haƙuri da haɗin kai domin ƙarfafa dimokuraɗiyya da zaman lafiyar ƙasa.