30/03/2026
HON. ALIYU NASIR KANKARA, CLN, MNLA
A wannan zamani da ake ƙara buƙatar shugabanci mai ma’ana a faɗin Najeriya, musamman a matakin ƙasa, fitowar matasa shugabanni irin su Aliyu Nasir Kankara na nuna sabon salo na shugabanci wanda zai haɗa kowa da kowa, kawo ƙirƙira da kuma mayar da hankali ga cigaban al’umma. Ƙudurinsa na tsayawa takarar wakilcin Karamar Hukumar Kankara a Majalisar Wakilai ta Jiha ya zo a kan lokaci, kuma ya ginu ne bisa hangen nesa na sauyi, haɗin kai da cigaba mai ɗorewa.
Aliyu Nasir Kankara ya fito a matsayin mutum mai nauyin hangen nesa, wanda tafiyarsa ta rayuwa ta nuna jajircewa, ladabi da kuma sadaukar da kai wajen hidimar jama’a. Duk da kasancewarsa matashi, yana da sabbin dabaru na rayuwa, wanda hakan ke ba shi damar haɗa kan manya da kuma matasa a Kankara da Jihar Katsina baki ɗaya.
A fagen aikinsa, ya taka rawa muhimmiya wajen shirye shiryen cigaban al’umma, ya rike muƙamai na shugabanci daban-daban, tare da ci gaba da fafutukar inganta rayuwar jama’a. Ta wannan hanya, ya samu ƙwarewa a fannoni da dama wanda ya haɗa da irin su; iya mu'amala tare da zama da jama’a, tattara goyon bayan al’umma, tsara dabaru, ƙarfafawa da kuma magance matsaloli waɗanda suke da matuƙar muhimmanci ga wakilci nagari a matakin majalisa.
A siyasance, Aliyu Nasir Kankara yana da cikakkiyar fahimta kan matsalolin da yankinsa na Kankara ke fuskanta, ciki har da rashin tsaro, rashin aikin yi, ƙarancin ababen more rayuwa da kuma matsalolin ilimi. Maimakon yin alƙawura marasa tushe, a shirye yake don samar da hanyoyin warware matsaloli cikin sauƙi, tare da jaddada haɗin gwuiwa da masu ruwa da tsaki, tsara manufofi masu amfani da kuma tabbatar da gaskiya da riƙon amana.
Aliyu Nasir Kankara yana da ƙuduri na musamman wajen ƙarfafa matasa maza da mata ta hanyar koyar da sana’o’i, tallafawa harkokin kasuwanci, noma, wasanni da samar da damarmaki. Yana hangen Kankara wadda ke cike da albarkatu inda matasa za su zama masu ƙirƙirar ayyukan yi, ba masu neman aiki kawai ba, tare da samun horo da kayan aiki da za su taimaka musu su yi gogayya a tattalin arziki na zamani. Manufofinsa sun haɗa da inganta ilimi, noma, ƙwarewar fasahar zamani da kuma koyon sana’o’i, domin tabbatar da cewa matasa ba'a bar su a baya a wannan zamani na fasaha ba.
Baya ga batun matasa, shirinsa ya haɗa da ƙarfafa tattalin arzikin ƙasa, inganta ababen more rayuwa a karkara, bunƙasa noma da kuma fafutukar samar da manufofi da za su inganta rayuwar talakawa. Kusancinsa da jama’a ya ba shi damar fahimtar ainihin buƙatun su, wanda hakan zai sa wakilcinsa ya zama mai tasiri da amfani.
A ƙarshe, Aliyu Nasir Kankara ba ɗan takara kawai ba ne, yana wakiltar sabon salo na shugabanci mai cike da hangen nesa, ƙwarewa da kuma ƙudurin yi wa jama’a hidima. Tsayawarsa takara wata dama ce ga Karamar Hukumar Kankara na rungumar shugabanci na matasa mai cike da ƙirƙira, kusanci da jama’a da kuma tabbatar da cigaba mai ɗorewa. Idan aka ba shi dama, yana da ƙwarewar da za ta kawo sauyi mai ma’ana ga Kankara da Jihar Katsina baki ɗaya.
Mustapha Muhammad Gimba,
Ɗan ƙasa mai kishin Karamar Hukumar Kankara, Jihar Katsina.