20/05/2026
Kotu ta bada umarnin kamo dan majalisar tarayya na Kumbotso, Idris Dankawu
Wata kotun majistare da ke Bwari a babban birnin tarayya Abuja ta bayar da sammacin k**a dan majalisar wakilai mai wakiltar ƙaramar hukumar Kumbotso a jihar Kano, Hon. Idris Dankawu, bisa zargin damfara wanda hakan ya saba wa sashe na 312 na kundin dokar laifuka( Penal Code).
Kotun tana ba da umarnin kamo dan majalisar ne nbayan wani korafi da kamfanin BAMZ Multi Essential Services ya shigar ta hannun lauyansa, Barrista Ahmad Umar Faroukh, yana neman a kamo dan majalisar saboda kin bayyana a gaban kotu.
Rahotanni sun nuna cewa ana zargin Dankawu da karbar kudin da s**a kai N77,035,069 ta hannun hadiminsa, Isma’il Yakubu Abubakar, wanda ake zargin ya karbi kudin bisa umarninsa.
A cikin korafin da lauyan mai kara, Barrista Ali Jamilu, ya gabatar, ya bayyana cewa Hon. Dankawu ya tuntubi kamfanin a ranar 18 ga Satumban 2025, inda ya yi alkawarin ba su kwangilar girka fitilu masu amfani da hasken rana da kudinta ya kai N77,035,069.
Lauyan ya ce an tura kudin zuwa asusun hadiminsa, Isma’il Yakubu Abubakar, amma ba a aiwatar da yarjejeniyar ba.
Korafin ya kuma bayyana cewa watanni takwas kafin hakan, Dankawu ya shaida wa kamfanin cewa ya samu kwangilar mazaba ta sany fitilun hasken rana kan tituna da kudinta ya kai N770,000,000, inda ya bukaci a biya kaso 10 cikin 100 na kudin kwangilar, wato N77,000,000, kafin a bayar da takardar kwangilar.
An ce an biya kudin ne a ranar 2 ga Oktoban 2025 zuwa asusun Access Bank na hadiminsa.
Sai dai bayan sama da watanni bakwai, ana zargin dan majalisar da hadimansa sun kasa bayar da kwangilar, suna ta bayar da dalilai mabambanta.
Lauyan mai kara ya kara da cewa bincike ya nuna babu wata irin kwangilar da aka bayar, kuma babu wata hujjar kashe kudin da za ta tabbatar da karbar kudaden.
An yi kokarin tuntubar Hon. Dankawu ko hadiminsa ya ci tura, domin wayoyinsu ba sa shiga.
Daily Nigerian Hausa