16/04/2022
ASHA RUWA A KOMA WASA
Bayan dan tak'aitaccen hutun da muka tafi sakamakon halin da kungiya ta shiga wanda ko wane memba da shugabanni sun san abun da yake faruwa.
To Alhamdulilah za6e dai anyi an gama kuma daman kuma haka tsarin yake ba zai yiwu ace kowa yayi nasara ba dole a samu wanda yayi nasara ko ta hanyar za6e ko ta wani abu daban.
Ina mai bawa wasu daga cikin "ya-yan wannan kungiya hakuri da azo a marawa wanda yayi nasara baya don cimma nasarar abun da mu ka saka a gaba. Wannan ba yana nufin ka aje jam'iyar ka ko ra'ayin ka na siyasa ba, kungiya tana nufin mu zama masu kawo ma wanda yayi nasara shawarar da za ta taimaki tafiyar mu, sannan idan za'ayi adawa ta kasance mai tsafta.
Daga karshe ina mai jajantawa wanda basu yi nasara ba Allah ya sa hakan shine mafi alheri, Allah ya kawo babban rabo zuwa gaba. Wanda s**a yi nasara ina maiyi masu addu'a Allah ya basu ikon sauke wannan nauyi da ya rataya a wuyan su, Allah yayi riko da hannayen su Ameen. Daga Jagoran wannan tafiya. Yakubu Sulaiman Kabobi