07/09/2026
Iyalan El-Rufai sun ba Janar Christopher Musa kwanaki bakwai ya janye kalamansa ko su garzaya kotu
Iyalan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, sun buƙaci ministan tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), da ya janye zargin da ya yi wa tsohon gwamnan na cewa ya shirya hallaka wasu mutane a kudancin Kaduna, ko kuma su ɗauki matakin shari'a a kansa.
A cikin wata sanarwar manema labarai da Hon. Mohammed Bello El-Rufai ya fitar a madadin iyalan a ranar Litinin a Abuja, ya bayyana cewa iyalan sun damu matuƙa da kalaman da ministan ya yi a ranar 3 ga watan Satumban 2026 yayin wani shirin kai-tsaye na "Politics Today" a gidan talabijin na Channels.