26/03/2022
MUDDIN AKA TSAYAR DA HON.AISHATU MB AHMAD KUMA ALLAH YA AMINCE MATA ,TO TABBAS ITA MAI IYA CIN ZABE NE.
Shi Mulki Allah idan yaga dama zai baka shine batare da la'akari da jinsinka ,addini, ko kuma kabilarka ba. Haka zalika idan ya baka bawai kafi kowa kwarewa bane ,inkuma ya hanaka bawai kafi kowa gazawa bane .
Misali cikin hukunci irinna ubangiji a shekarar 2019 Alh.Ibrahim Hassan Dankwambo ko kaine hasidun iza hasada kasan cewa yafi abokin takararsa kwarewa,Ilimi,farin jini,karbuwa,chanchanta,da karfin iko amma da Allah ya tashi hukunci irin nasa sai yabaiwa 'Dan Alkali nasara badon yafi Dankwambo da komai ba.
Nayi wannan bayanine domin na jawo hankalin shugabannin jam'iyyar PDP musamman akaramar hukumar Akko da cewa shi faduwa a zabe kocin zabe wasu lokutan bawai suna nuna rashin nagartan 'Dan takara bane ,domin da rashin nagartan 'Dan takarane kawai ke jawo faduwa zabe da lallai Dankwambo bai fadi ba a zaben shekarar 2019 .
Ko shakka babu rashin nasarar jam'iyyar PDP a zaben majalisar tarayya mai wakiltar Akko a shekarar 2019 yanada nasaba da rigingimun cikin gida bawai rashin nagarta daga 'yar takarar mu ba ,wanda ko kaki Allah kasan hakan ya faru kuma bama fata hakan ya sake faruwa Insha Allahu.
Lallai Hon.Aishatu MB Ahmad ta chanchata ta kowani bangare domi tanada rikon amana irin na siyasa ,ta taimaki al'umma da dama kuma tayiwa jam'iyyar PDP rikon gaske lokacin da jam'iyyar keda bukatan hakan , tanada ilimi da gogewar da zata iya tashi ta gabatar da kuduri akan al'ummar ta koda kuwa a majalisar dinkin duniya ne ,Hon.Aishatu MB Ahmad mace ce da Allah ya h**e mata farin jinin da zata iya cin zabe a kowani mataki domin al'umma na tare da ita.
A irin ra'ayi nawa zan iya cewa a matakin kujerar majalisar tarayya lallai ba bukatan chanza 'yar takara sai dai kawai neman hadinkan 'ya'yan jam'iyya .
Allah ya bamu ikon biyayya ga duk wanda Allah ya baiwa nasara a zaben fidda gwani .
Ahmad Abdullahi Deputy✍️
Sat 26,March 2022.