13/04/2022
A. A. Zaura: Jumma’a Mai Kyau…
Rahotanni masu inganci daga kowane lungu da sako na Jihar Kano, musamman a farfajiyar siyasa, suna nuni kan cewa, ba a taba yin wani dan siyasa mai dama, ba shi da damuwa, kamar Alhaji Abdulsalam Abdulkareem Zaura, wanda aka fi sani da A. A. Zaura ba. Wannan ya kara tabbatar da cewa Juma’a mai kyau, tun daga Laraba masu hankali ke gane ta!
Hakika, wata guguwa mai cike da launin canji na alheri ke rururwa a babbar birni, da har ta a kullum ake ganin tagomashin Alhaji A. A. Zaura da yunkurinsa na ganin an cimma nasara.
Bisa ga dukkan alamu, siyasar shekarar 2023 ta matasa ce, su ne ake ganin za su fi kowa taka mahimmiyar rawa a cikinta, saboda yadda shi ma kansa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, a shekarun baya, ya marawa kudurin da tawagar wasu matasa s**a mika masa na a ba wa matasan dama su taka rawa a fagen mulki.
Shin wane ne Alhaji Abdulsalam Abdulkareem Zaura?
- Idan kana son fassara wannan bawan Allah, tilas ka tanaji wasu kyawawan kalmomi masu dangogin alheri!
- Idan kai matashi ne, to ka sani cewa sami abokin tafiya a wajen Zaura!
- Idan kuma kai dattijo ne, shakka babu, ka sami da-nagari mai biyayya ga iyaye, mai neman albarkar iyaye, mai tsananin girmama nag aba da shi.
- Idan kuma dan kasuwa ne kai, ko tantama babu, kana da abokin huldayyar kasuwanci!
- Idan kai matashi ne mai son wanka da kwalliya, to, ka sani ka zo gidanta!
A. A. Zaura matashi ne mai sanyin rai, mai hangen nesa, mai dubun-dubatar basira, wanda Allah Ta’ala Ya huwace ma sa ayyuka da dama. Wadanda s**a san Zaura, za su fada maka cewa gabanin shigarsa harkar siyasa ne, yake kan gaba wajen yi wa al’ummarsa hidima ta fuskoki da daman gaske. Ya riki harkar kasuwanci, tun lokacin da yake karatu a makarantar Sakandare.
A takaice dai, Alhaji Abdulsalam Zaura mutum ne mai dimbin basira da fasaha ta zamani, musamman ma, da ya shiga jami’a, ya sami digiri kan sha’anin mulki da tattalin arziki. A nan, ma ya yi zarra, inda kuma yake tunanin ya sanya karatunsa a aikace idan har Allah Ta’ala Ya ba shi damar samun nasara a zabukan da za a yi nan gaba a shekarar 2023.
Muradinsa ga Kanawa: A nan dai, ko ba a ce komai ba, A. A. Zaura ya karanci dukkanin lamura da jihar ke bukata a yau. Sannan daga cikin manyan muradunsa dai, yana da kudurin dorawa daga inda Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya ajiye ayyukansa na alheri.
A kodayaushe za ka ji yadda Alhaji Zaura ke yabawa kokarin da wannan gwamnati mai ci ke yi a harkar mulki da yunkurin farfado da darajar Jihar Kano masu albarka. Hakan ce ta sanya a yanzu, yake da muradin ci gaba da gyara fasalin Jihar Kano, domin ya tabbatar Kanawa sun ji dadin harkar mulkinsa, idan Allah Ya tabbatar.
Wannan makalar ba za ta iya daukar muradun A. A. Zaura masu mahimmanci ba, amma manazarta dai sun yi amanna cewar kusan dukkanin ‘yan takarkarun da s**a fito, muradun Zaura sun fi haskawa, kuma sun fi samun karbuwa ga Kanawa ciki da waje.
Abin da ya rage dai shi ne, kamar yadda muka sani Jumma’a ce babbar rana a duk ranaku, ashe Kenan ya zama wajibi mu tsimayi wannan babbar ranar!