KEBBI RADIO

KEBBI RADIO ...The Rising Star.... Kalgo Road Birnin Kebbi

Gwamnatin Kebbi ta goyi bayan aikin tantance bayanai na hukumar Gwamnatin Jihar Kebbi ta tabbatar da shirinta na bai wa ...
07/05/2026

Gwamnatin Kebbi ta goyi bayan aikin tantance bayanai na hukumar

Gwamnatin Jihar Kebbi ta tabbatar da shirinta na bai wa Hukumar Rarraba Kudin Shiga da Kasafin Kudi ta Tarayya (RMAFC) cikakken hadin kai domin gudanar da aikin tantance bayanai kan rabon kudaden shiga a fadin kasa.

Mataimakin Gwamnan jihar, Sanata Umar Abubakar Tafida, ne ya bayyana haka yayin karbar tawagar hukumar da kwamitin FAAC a Birnin Kebbi.

Ya ce gwamnatin jiha ta fahimci muhimmancin sahihan bayanai wajen tabbatar da adalci wajen rabon kudaden shiga ga jihohi da kananan hukumomi.

Tafida ya kara da cewa Gwamna Nasir Idris ya umarci Ma’aikatar Kudi, Hukumar Tattara Haraji, shugabannin kananan hukumomi da sauran ma’aikatu da su bai wa tawagar cikakken hadin kai.

Shugaban tawagar, Farfesa Olusegun Adekunle Wright, ya ce aikin na da muhimmanci wajen sabunta bayanan da ake amfani da su wajen rabon kudaden shiga domin dacewa da sauye-sauyen tattalin arziki da ci gaba.

Itama Kwamishiniyar RMAFC, Hajiya Rakiya Tanko Ayuba, ta yabawa gwamnatin Kebbi bisa goyon bayan da take bai wa hukumar tare da neman a ware mata fili domin gina ofishin hukumar a jihar.

Gwamnatin Jihar  Kebbi ta kaddamar da sabbin ayyukan lafiya a Birnin Kebbi da KalgoGwamnatin Jihar Kebbi ta kaddamar da ...
07/05/2026

Gwamnatin Jihar Kebbi ta kaddamar da sabbin ayyukan lafiya a Birnin Kebbi da Kalgo

Gwamnatin Jihar Kebbi ta kaddamar da gyaran da fadada sashen gaggawa na Asibitin Sir Yahaya Memorial da ke Birnin Kebbi tare da sabon gyaran dakin ajiye gawa na Asibitin Koyarwa na Jihar Kebbi (KSTH) da ke Kalgo.

Kwamishinan Lafiya na jihar, Alhaji Ismail Yakubu Augie, wanda ya wakilci Gwamna Nasir Idris wajen mika ayyukan, ya ce gwamnatin jihar na ci gaba da ba bangaren lafiya muhimmanci domin inganta kula da lafiyar al’umma.

Ya bayyana cewa an gudanar da gyaran ne domin kara inganta ayyukan asibitocin da kuma cika sharudan amincewa da horas da daliban likitanci na Jami’ar Abdullahi Fodio da ke Aliero.

Kwamishinan ya kuma bayyana cewa gwamnati ta samar da hasken rana ta hanyar kafa fitilun sola sama da 120 a harabar asibitin Kalgo, tare da samar da na’urar lantarki mai amfani da hasken rana domin tabbatar da wadataccen wuta a dakin ajiye gawa.

Shugabannin asibitocin sun yabawa Gwamna Nasir Idris bisa tallafin da yake bai wa bangaren lafiya tare da alkawarin kula da sabbin kayayyakin yadda ya kamata.

By Hassan Garba BuhariThe Executive Secretary of Kebbi State Contributory Healthcare Management Agency, Dr. Murtala Muha...
07/05/2026

By Hassan Garba Buhari

The Executive Secretary of Kebbi State Contributory Healthcare Management Agency, Dr. Murtala Muhammad Dandare, has intensified efforts to expand healthcare coverage in Kebbi State by advocating for the establishment of zonal offices and the commencement of employer contributions for civil servants under the state health insurance scheme.

Dr. Dandare made the appeal during a familiarization visit to the Kebbi State Ministry of Health as part of a broader stakeholder engagement tour aimed at strengthening collaboration and support for the Agency’s mandate.

According to the Executive Secretary, the establishment of zonal offices would improve the Agency’s reach and enhance access to healthcare services across the state, while the commencement of employer contributions would strengthen the implementation of the contributory healthcare scheme for civil servants.

As part of the tour, Dr. Dandare also visited the Department of State Security Services, where he emphasized the need for stronger security collaboration to ensure the safety of KECHEMA staff carrying out official assignments within and outside Birnin Kebbi.

Responding, the Commissioner for Health, Alhaji Yakubu Samaila Augie, and the DSS Director in Kebbi State, represented by Deputy Director of Operations, Mr. Jamilu, commended the initiative and assured the Agency of their continued support.

Dr. Dandare was accompanied on the visits by the Chairman of the KECHEMA Governing Board, Comrade Abubakar Bala Gado Kamba, alongside members of the board and the Agency’s management team.

The statement was signed by Mansur Danjuma Sanchi, Public Relations Officer of KECHEMA.

07/05/2026

Kanun Labarai

Arsenal da PSG za su fafata a wasan karshe nacin kofin zakarun Turai ta bana.Kungiyar Arsenal za ta kara da Paris Saint-...
07/05/2026

Arsenal da PSG za su fafata a wasan karshe nacin kofin zakarun Turai ta bana.

Kungiyar Arsenal za ta kara da Paris Saint-Germain a wasan karshe na gasar zakarun nahiyar Turai ta bana, a fafatawar da ake sa ran za ta kayatar matuka.

Arsenal na neman lashe kofin karo na farko cikin sama da shekaru 20 da ta dade tana jiran wannan dama, yayin da PSG ke kokarin kare martabarta tare da komawa Paris da kofin.

Masu sharhi na ganin wasan zai kasance mai zafi da cike da dabaru, musamman yadda kungiyoyin biyu s**a nuna bajinta tun daga matakin rukuni har zuwa wasan kusa da na karshe.

Gwamnatin Tarayya ta haramta amfani da kalmar “Dr” ga masu Digirin girmamawaGwamnatin Tarayya ta hana masu digirin girma...
07/05/2026

Gwamnatin Tarayya ta haramta amfani da kalmar “Dr” ga masu Digirin girmamawa

Gwamnatin Tarayya ta hana masu digirin girmamawa (Honorary Degree) amfani da taken “Dr” a gaban sunayensu a duk wata mu’amala.

Ministan Ilimi, Tunji Alausa, ya bayyana cewa hakan na yaudarar jama’a tare da bata martabar cancantar ilimi.

Ya ce daga yanzu duk wanda ya karya wannan doka zai fuskanci hukunci bisa zargin zambar ilimi.

Sankarau yayi sanadiyar mutuwar yara 33 a  SokotoGwamnatin Jihar Sokoto ta tabbatar da mutuwar yara 33 sakamakon barkewa...
07/05/2026

Sankarau yayi sanadiyar mutuwar yara 33 a Sokoto

Gwamnatin Jihar Sokoto ta tabbatar da mutuwar yara 33 sakamakon barkewar cutar sankarau (cerebrospinal meningitis) a wasu sassan jihar. Hukumomi sun bayyana cewa ana ci gaba da daukar matakan dakile yaduwar cutar tare da wayar da kan al’umma kan hanyoyin kariya.

Gwamnati ta ce ba za ta dawo da Tallafin mai baGwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ba ta da shirin dawo da tallafin man fe...
07/05/2026

Gwamnati ta ce ba za ta dawo da Tallafin mai ba

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ba ta da shirin dawo da tallafin man fetur ko ƙayyade farashinsa a kasuwa.

Ministan kuɗi, Taiwo Oyedele, ya bayyana hakan yayin wata ganawa da ‘yan kasuwa na duniya a Faransa tare da Shugaba Bola Tinubu.

Ya ce gwamnati za ta ci gaba da barin kasuwa ta kayyade farashin mai domin bunƙasa tattalin arziki da ƙara jawo hannun jari.

Hukumar Ilimin Bai Ɗaya ta Jihar Kebbi (SUBEB) tare da haɗin gwiwar Hukumar Ilimin Bai Ɗaya ta Ƙasa (UBEC) sun gudanar d...
07/05/2026

Hukumar Ilimin Bai Ɗaya ta Jihar Kebbi (SUBEB) tare da haɗin gwiwar Hukumar Ilimin Bai Ɗaya ta Ƙasa (UBEC) sun gudanar da taron horaswa na kwanaki biyu ga malamai da masu kula da harkokin ilimi kan sabon tsarin manhajar ilimin bai ɗaya da aka sabunta.

Taron wanda aka gudanar daga ranar 6 zuwa 7 ga Mayu, 2026 a Makarantar Atiku Bagudu Science Model Primary School, ya haɗa shugabannin makarantu, jami’an ilimi da sauran masu ruwa da tsaki daga sassan jihar.

Shugaban SUBEB, Farfesa Sulaiman Khalid, ya bayyana cewa sabon tsarin manhajar zai taimaka wajen bai wa ɗalibai ƙwarewar zamani da ta dace da ƙarni na 21, musamman ta hanyar saka darussan kwamfuta a dukkan matakan karatu.

Ya ce daga yanzu duk koyarwa da jarabawa za su bi sabon tsarin manhajar, yana mai gargadin malamai da su guji koyar da tsofaffin darussa marasa amfani.

Farfesa Khalid ya kuma buƙaci makarantu masu zaman kansu su shiga cikin shirin domin tabbatar da kowa ya amfana da sabon tsarin.

A nasa jawabin, mamba na hukumar SUBEB, Dakta Usman Na’Allah Bunza, ya yabawa gwamnatin jihar da shugabancin SUBEB bisa ƙoƙarin inganta ilimin bai ɗaya a jihar.

Shi ma Daraktan Sashen Ayyukan Ilimi, Alhaji Faruku Salihu Koko, ya ce an shirya horaswar ne domin ƙara wa malamai ilimi da dabarun aiwatar da sabon tsarin manhajar yadda ya kamata.

Masu halartar taron sun bayyana aniyarsu ta amfani da ilimin da s**a samu tare da koyar da sauran malamai a makarantunsu.

The pilgrims of Birnin Kebbi local government have been advised to abide by rules and regulations of NAHCON and  PWA  fo...
07/05/2026

The pilgrims of Birnin Kebbi local government have been advised to abide by rules and regulations of NAHCON and PWA for a successful Hajj exercise

The call was made by the Executive chairman of the State pilgrims Welfare Agency Alh. Faruku Musa Yaro .while addressing four hundred and twenty nine intending pilgrims that made up third flight.

Alh. Faruku Enabo explained that the State government under the leadership of Dr. Nasir Idris Kwauran Gwandu has paid Hadya to all Kebbi State pilgrims

He said the wife of the State Governor Hajiya Nafisa Nasir Idris has equally provided Ihram, soap, and slippers to all the female Pilgrims

Enabo father said Governor Nasir Idris has directed all political leaders and appoities to Financially assist the pilgrims from their respective areas.

In his speech the State Amir Hajj retired Controller General Nigeria Correctional Service Ahmad Jafar Jega advised the pilgrims to be good ambassadorrs of the State and Nigeria in t general at the Holy Land.

Jafar also callled on pilgrims to be hyegenic and flush Toilet after use.

Speaking Earlier the State commissioner for Religious Affairs Alh.Sani Aliyu Zuru said the State pilgrims have been tought on all Hajj obligations.

He therefore advised them to avoid any wrong act capable of spoiling their Hajj .

The  APC Aspirrant vying for the  seat of the State House  of  Assembly  for Suru Constituency   says Youth empowerment ...
07/05/2026

The APC Aspirrant vying for the seat of the State House of Assembly for Suru Constituency says Youth empowerment and people oriented projects will receive his priority.

Alh.Umar Maigandi Dakingari stated this while submitting his nomination form at APC State Secretariat Birnin kebbi.

He expressed confidence that the state Governor and APC Stake holders will do justice to all Aspirant's.

Alh Umar called on all APC Aspiranntts to be loyal to the party by supporting any one emerged as candidate in all the posts to be contested.

Receiving the nomination form the national committee on sales and collection of nomination forms under the leadership of Alh.Bashir Inuwa assured Justice for all.

Address

Klm 8 Birnin Kebbi/Kalgo Road

KEBBISTATE

Opening Hours

Monday 06:00 - 23:46
Tuesday 06:00 - 23:45
Wednesday 06:00 - 23:45
Thursday 06:00 - 23:45
Friday 06:00 - 23:45
Saturday 06:00 - 23:45
Sunday 06:00 - 23:45

Telephone

+2348062213150

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KEBBI RADIO posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to KEBBI RADIO:

  • Want your organization to be the top-listed Government Service?

Share