15/09/2020
🎃YAR ♡ TALAKAWA🎃
Bismillahil rahmanil rahim"
Tafe nake a cikin wata kasuwar fruits(kayan marmari),nazo wuce wata rumfa,mai dauke da kayan marmari kala kala, wata kyakkyawar yarinya na hango a ciki, sanye take da wasu kodaddun atamfa riga da skirt,yarinyar ba zata wuce shekaru sha shidda ba, sai tsalle take tana fadin, kuzo ku siya, namu sunfi zaki, tana maganar fuskar ta dauke da murmushi,kumatun ta sun lotsa, mutane dayawa s**a tsaya a wurin suna kallon ta,kwanin sha'awa, gata kyakkyawa, ta dauko lemu,ta dauko alaba da sauran fruits din, tana fadi musu anfanin su,dan kawai su siya.Ni afrah nace bari na bi wannan yarinya mai siyar da kayan marmari, dan kwaso wa masoyana labari.Wani mutuni na gani ya kira ta ciki, yarinyar na murmushin mai kara mata kyau, tace ya habu har zamu tashi ne, naga akwai sauran jama'a a kasuwar, mu dan kara jira kaji, ya habu ya kalle ta yace NI'IMATU, ke bakya gajiya ne , tun safe k**e tsalle tsallen nan, niimatu ta dara, ta kai wa ya habu naushi a hannu, ni ban gaji ba Allah, mudan kara jimawa kaji, ya habu yayi dariya, ke kam da namiji ce , da anyi jarumi.Niimatu ta daure fuska, ohh ni yanzu ba jaruma bace ashe ko? Ta turo masa dan karamin bakin ta, ya habu yadan dungurar mata da kai, yace a tsalle tsallen k**e jaruma, ya wuce waje abunsa, niimatu taja tsaki, sannan ta murmusa itama ta bishi wajen. Umma !umma! Ina k**e gamu mu dawo, umma ta fito cike da fara'a, niimatu tayi saurin ajiye ledar hannunta,tayi wurin umman ta rungume ta, umma tayi murmushi, niimatu bakya girma ko?, niimatu tayi murmushin ta, tana kallon umman tace, umma idan dai a gaban kine ni har yanzu yarinya ce karama, koda na haifi yara dari ne, umma tayi dariya , ya habu ya karaso ciki, yace umma sannu da gida?, umma tace ko keda sannu habu.Sunyi wanka sun ci abinci, suna zaune dan tsakar gidan su, wanda ko siminti babu,ga ginin gidan duk ya lalace duk da na bulo ne, amma da yake ya tsofa, duk ya zaizaye.Ya habu yasa hannu cikin aljihun sa, ya fiddo wasu yan kudi, ya mikawa umman, ga wannan nasan malam sahabi yazo, umma tace yazo kuwa dazun da rana, dama yace gobe idan munsan bamu da kudin hayan , toh kada mu sake ya iske mu anan, ya habu ya girgiza kai, Allah yana sane damu, kuma mun gode masa, daya barmu da ranmu da kuma lafiyar mu ,umma tace aini har yanzu ina nan ina wa bawan Allah nan daya baka rumfa , kuma ya baka kudin jarin nan addu'a, dan ba karamin taimakon mu yayi ba ,Ya habu yace nima ina masa addu'a har yanzu, umma.Niimatu dake kwance kanta bisan cinyan umma, tana barci,sai munshari take, tana juye juye ,ya habu ya tafka mata bugu a baya, kee uwar munshari tashi ki koma daki. Niimatu ta mike ta kura masa ido tana smiling, ya habu yaja tsaki, ke wai bakya gajiya da murmushi ne, kumatun ki baya gajiya?, umma tace kyele ta habu ta huta, ba karamin kokari take ba, niimatu tace nifa ba barci nake ba yaya, kuma yaushe nayi munshari?, ya habu ya mike yace umma sai da safe, ke kuma , ya nuna niimatu, saura kiyi ta barci, kada ki tashi ki shirya da wuri, niimatu ta washe baki, ta nuna kanta nifa jaruma ce yaya.... ya habu yayi dan tsaki ya fice abunsa, dan idan zai biye wa niimatu bazai samu barcin kirki ba....