15/03/2026
An haifi wata jaririya wadda idanunta suke a rufe gaba ɗaya tun daga haihuwa. Likitoci sun bayyana cewa ana buƙatar tiyata domin buɗe idanun nata, amma kuɗin da ake nema ya kai dala $5,000, alhali iyayenta ba su da halin da za su iya biyan wannan kuɗi.
Lokacin da aka sanar da Nasir El-Rufai da matarsa halin da iyayen jaririyar ke ciki, bai ɗauki lokaci ba kafin ya nuna tausayi. Ba wai ya tsaya kan adadin kuɗin da ake buƙata kawai ba, sai ya ƙara musu har zuwa dala $8,000 domin su samu damar tafiya Indiya a yi wa jaririyar tiyata yadda ya k**ata.
Wannan lamari ya sake nuna cewa shugabanci na gaskiya ba wai iko ko mukami kawai ba ne. Akwai tausayi, jin ƙai, da kuma niyyar taimaka wa al’umma, ko da kuwa ba tare da an yi hayaniya ko tallatawa ba. Sau da yawa irin waɗannan ayyukan alheri suna faruwa ne a ɓoye, amma tasirinsu yana canza rayuwar mutane.
Sir Usman Babajo ne ya rawaito wannan labari, inda ya ce Ja’afar Muhammed Bello ne ya ba shi labarin. Haka kuma, a baya ma an ruwaito cewa Malam da wasu manyan shugabanni suna da halin zuwa asibitoci cikin dare su biya kuɗin maganin marasa lafiya ba tare da kowa ya sani ba.
Irin waɗannan misalai suna tuna mana cewa aikin alheri ko da an yi shi a ɓoye, wata rana gaskiya kan bayyana. A saboda haka ne El-Rufai Live ke kira ga jama’a da su yi koyi da irin waɗannan kyawawan halaye na taimakon juna da jin ƙai ga al’umma.