15/05/2026
Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Alhaji Ahmad Aminu Yar’adua, ya shiga jerin manyan ‘yan siyasar da s**a nuna aniyar su ta neman kujerar gwamnan Jihar Katsina a babban zaɓen shekarar 2027, bayan da ya sayi fom ɗin tsayawa takara a ƙarƙashin jam’iyyar ADC.
Rahotanni sun bayyana cewa matakin da Alhaji Ahmad Aminu Yar’adua ya ɗauka na sayen fom ɗin takara ya ƙara dumama harkokin siyasa a jihar Katsina, musamman ganin yadda yake da ƙwarewa da gogewa a harkokin mulki da gudanar da gwamnati.
Alhaji Ahmad Aminu Yar’adua, wanda ya taɓa riƙe muƙamin Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, ana kallon sa a matsayin ɗaya daga cikin fitattun ‘yan siyasar jihar da s**a daɗe suna taka rawa wajen ci gaban siyasa da gudanarwar gwamnati. Masu bibiyar al’amuran siyasa na ganin fitowarsa takara a ƙarƙashin ADC zai kawo sabon salo da gasa a siyasar jihar kafin zaɓen 2027.
Wasu magoya bayan jam’iyyar ADC sun bayyana farin cikin su kan matakin da tsohon sakataren gwamnatin ya ɗauka, inda s**a ce suna da yaƙinin cewa gogewar sa da fahimtar sa kan harkokin mulki za su taimaka wajen samar da shugabanci nagari idan har ya samu nasarar lashe zaɓen.
A gefe guda kuma, masu sharhi kan harkokin siyasa sun bayyana cewa shigowar Ahmad Aminu Yar’adua cikin tseren neman kujerar gwamna zai iya sauya yanayin siyasar jihar Katsina, musamman a daidai lokacin da jam’iyyu daban-daban suke ci gaba da shirye-shiryen tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.
Ana sa ran nan gaba kaɗan ɗan takarar zai bayyana manufofin sa da tsare-tsaren da yake da su domin ci gaban Jihar Katsina da walwalar al’ummar jihar idan har aka ba shi dama ya jagoranci jihar.