17/05/2026
All Progressives Congress Ta Tabbatar da Abubakar Kabir Abubakar a Matsayin Ɗan Takarar Kujerar Majalisar Wakilai ta Bichi
Honarabul Abubakar Kabir Abubakar ya zama zaɓaɓɓen ɗan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) guda ɗaya tilo domin neman kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar Bichi Federal Constituency a zaɓen shekarar 2027.
A ranar Asabar, 17 ga Mayu, 2026, jam’iyyar APC ta fara gudanar da zaɓukan fidda gwani na ‘yan takarar Majalisar Wakilai a faɗin ƙasar nan, inda Hon. Abubakar Kabir Abubakar ya samu nasara bayan shugabannin jam’iyyar APC na dukkanin wards 11 na Bichi Federal Constituency s**a amince da shi a matsayin ɗan takara ba tare da hamayya ba.
Da yake jawabi yayin taron tabbatarwar, Bola Ahmed Tinubu wanda wakilinsa shi ne mai ba shi shawara kan harkokin siyasa, Ibrahim Kabir Masari, ya bayyana wakilcin Abba Bichi a matsayin mai kusanci da al’umma, mai sauraron jama’a tare da kawo ayyukan ci gaba, musamman ayyukan mazabu da shirye-shiryen tallafawa matasa.
Masari ya bayyana cewa duk da APC na gudanar da zaɓukan fidda gwani a faɗin ƙasa, mazabar Bichi tana daga cikin wuraren da s**a fi jan hankali saboda ayyukan ci gaba da kuma kyakkyawar alaƙar da ɗan majalisar ke da ita da al’umma.
Taron ya samu halartar manyan jiga-jigan APC ciki har da Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf; Hon. Sada Soli mai wakiltar mazabar Jibia/Kaita; da Ministan Gidaje da Raya Birane, Engr. Mu’azu Rabi’u Darma, tare da sauran shugabannin jam’iyya.
Sauran waɗanda s**a halarta sun haɗa da Manajan Darakta na Hadejia Jama’are River Basin Development Authority, Rabiu Suleiman Bichi; tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Abdullahi Baffa Bichi; Shugaban Ƙaramar Hukumar Bichi; shugabannin mata; shugabannin matasa; da sauran masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na jihar Kano.
A jawabinsa, Abba Kabir Yusuf ya yaba da irin wakilcin da Hon. Abubakar Kabir Abubakar ke yi tun bayan zaɓensa zuwa Majalisar Wakilai a shekarar 2019.
“Ina yaba wa Hon. Abubakar Kabir Abubakar bisa kyakkyawan wakilci da yake yi. Tun daga shekarar 2023 nake addu’ar samun damar yin aiki tare da shi domin cigaban Bichi da Jihar Kano,” in ji Gwamna Yusuf.
Ya kuma bayyana ayyukan mazabarsa a matsayin abin a yaba, musamman a bangaren tallafawa matasa da ayyukan ci gaban al’umma.
Gwamnan ya kuma yi kira ga al’ummar Bichi da su sake zaɓen Abubakar Kabir Abubakar a zaɓen 2027, yana mai bayyana ƙwarewarsa da jajircewarsa wajen hidimtawa jama’a.
Tun da farko a jawabinsa, Abubakar Kabir Abubakar ya gode wa Allah Maɗaukakin Sarki bisa samun damar zama ɗan takarar APC na mazabar Bichi, tare da alƙawarin ci gaba da aiki domin ci gaban al’ummar mazabar idan aka sake zaɓensa a 2027.
Abubakar Kabir, wanda shi ne Shugaban Kwamitin Kasafin Kuɗi na Majalisar Wakilai, ya sake jaddada ƙudirinsa na cigaban Ƙaramar Hukumar Bichi.
Ya kuma yaba wa Bola Ahmed Tinubu bisa ayyukan manyan tituna da ake gudanarwa a Arewacin Najeriya da Jihar Kano, ciki har da aikin hanyar Kano–Daura, Abuja–Kaduna–Kano, da Kano–Maiduguri.
Har ila yau, ya yaba da shirin aikin layin dogo na Kano Metropolitan Rail Service na naira tiriliyan ɗaya, wanda ake sa ran zai inganta sufuri, bunƙasa tattalin arziki da rage cunkoson ababen hawa a birnin Kano.
Hon. Abubakar Kabir Abubakar ya tabbatar da cewa al’ummar Ƙaramar Hukumar Bichi, mai sama da masu kaɗa ƙuri’a 300,000, za su ci gaba da mara wa Bola Ahmed Tinubu da APC baya domin samun nasara a zaɓen 2027.