22/03/2026
LABARAI KAN RIKICIN PDP DA RAWAR INEC
Muna son jawo hankalin ‘yan Najeriya kan wasu abubuwa masu tayar da hankali da wasu ‘yan jam’iyyar People’s Democratic Party (PDP) da ke nuna rashin haɗin kai suke aikatawa, waɗanda ake zargin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT) kuma abokin hulɗar Bola Ahmed Tinubu ne ke jagoranta, domin kokarin rusa tsarin doka da kundin tsarin jam’iyyar ya tanada.
Ya kamata a fayyace ba tare da wata shakka ba cewa:
Hukuncin baya-bayan nan na Kotun Ɗaukaka Ƙara (Court of Appeal) ya soke abin da ake kira taron Ibadan (Ibadan convention), tare da tabbatar da dakatarwar wasu mambobin Kwamitin Gudanarwa na Ƙasa (National Working Committee – NWC). Wadannan mutane, bisa doka da kundin tsarin PDP, ba su da wata hurumi ko ikon shirya ko shiga duk wata harkar jam’iyya.
Haka kuma, kotun ta ladabtar da wani lauya na PDP da aka dakatar, saboda yin aiki a madadin jam’iyyar ba bisa ka’ida ba, lamarin da ke ƙara tabbatar da cewa dole ne a mutunta doka da kundin tsarin jam’iyya a kowane lokaci.
KAN SHUGABANCI DA HALALCI
Kundin tsarin PDP ya bayyana a sarari cewa:
A irin wannan yanayi, alhakin shugabanci yana hannun Kwamitin Amintattu (Board of Trustees), wanda ke karkashin jagorancin Adolphus Wabara.
Wannan kwamiti har yanzu yana nan daram, ana ganinsa a hukumance, kuma ya riga ya fara kokarin sasanta bangarori domin samar da fahimtar juna.
Saboda haka:
Babu gibin shugabanci a PDP
Babu wani dalili da zai ba da hujjar kafa wasu majalisu ko tsarin da ba su dace da doka ba
Duk wani yunkuri na kafa bangarori (factions) sabawa kundin tsarin jam’iyya ne, ba shi da inganci, kuma yana da manufar ta siyasa a ciki.
TAMBAYOYI GA INEC
Muna kira ga Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da ta gaggauta bayyana matsayinta a fili:
Mene ne matsayin shugabancin PDP a hukumance?
Shin ayyukan wadannan bangarori suna da sahalewa ne ko kuwa ba bisa ka’ida ba ne?
Shin INEC ta amince ko ta yi rajistar wata sabuwar jam’iyya da ke da alaka da wadannan da ke nuna rashin jin dadi?
‘Yan Najeriya na da hakkin sanin gaskiya. Yin shiru daga bangaren INEC na haifar da damuwa da kuma sanya shakku a zukatan jama’a.
SABANI A MATSAYIN INEC
Yana da muhimmanci a bayyana cewa, a shafin hukuma na Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), har yanzu ana nuna shugabancin PDP na karshe da aka amince da shi a karkashin Shugaban Jam’iyya na riko, Umar Iliya Damagum.
Wannan ya haifar da tambaya mai muhimmanci:
Idan har bayanan INEC na hukuma suna nuna wannan shugabanci, me ya sa ake ganin hukumar tana sa ido ko kuma tana amincewa da ayyukan wani tsari na rikon kwarya da aka kafa ba bisa ka’ida ba?
Ba zai yiwu INEC ta rika daukar matsayi biyu a lokaci guda ba. Ba za ta iya nuna wani matsayi a hukumance, amma a aikace ta yi wani abu dabam ba.
Dole ne INEC ta kasance mai zaman kanta kuma mai adalci — ba kayan aiki na wata jam’iyya mai mulki ba.
KARIN MUHIMMIYAR TAMBAYA GA INEC
Har ila yau, muna tambayar wata muhimmiyar tambaya:
Shin yanzu INEC tana kafa wani sabon tsari ne inda duk wani dan jam’iyya da bai gamsu ba zai iya kafa bangare, ya dauki iko, sannan ya yi tsammanin INEC za ta amince da shi ko ta kula da ayyukansa?
Idan haka ya zama al’ada, hakan na nufin ana halasta rikici tare da rusa tsarin dimokuradiyya na cikin gida na jam’iyyu.
Jam’iyyun siyasa suna tafiya ne bisa kundin tsarinsu da dokokin kasa — ba bisa bukatun kai tsaye ko ra’ayin mutum daya ba. Bai kamata INEC ta haifar ko ta karfafa yanayi da zai sa saba doka ya zama abin da aka saba ba.
SAKON KARSHEN DA YA KE DA KARFI
INEC dole ta fito fili:
Ba za ta halasta abin da ba bisa ka’ida ba a yau, sannan ta ce tana kare dimokuradiyya gobe ba.
KIRA GA SAURAN JAM’IYYUN SIYASA
Muna kira ga sauran jam’iyyun siyasa da aka yi wa rajista a Najeriya da kada su yi shiru kan wannan lamari. Yin shiru a irin wannan lokaci ba nuna tsaka-tsaki ba ne — nuna goyon baya ne kai tsaye.
Yawancin wadannan jam’iyyun suna da shari’o’i a gaban Kotun Ɗaukaka Ƙara da Babbar Kotun Tarayya. Ya kamata su fahimci cewa abin da ke faruwa ga PDP a yau, zai iya faruwa ga kowace jam’iyya gobe.
Wannan batu ba na jam’iyya daya kadai ba ne, batu ne na kare dimokuradiyya, bin doka, da mutuncin cibiyoyi.
Muna kira ga dukkan jam’iyyun siyasa da su tashi tsaye, su wuce bambancin ra’ayi na siyasa, su kare sararin dimokuradiyya.
Raunin jam’iyya daya, raunin dukkan jam’iyyu ne!
MATSAYINMU NA KARSHE
Muna gargadin duk wani yunkuri na kokarin raunana PDP domin biyan bukatun wasu na siyasa daga waje. ‘Yan Najeriya na kallo.
Jam’iyyar People’s Democratic Party har yanzu babbar jam’iyya ce mai karfi, kuma babu wani mataki na cin amana daga ciki ko tsoma baki daga waje da zai iya rusa tubalinta.
K. Media