12/06/2022
BABBAN KIRA ZUWA GA MUTANEN AREWA MUSULMAI
Wannan kiran ya shafeni, ya shafeka, ya shafi iyalanka da 'yan uwanka da kowa naka game da makomar Nigeria
Sanin kanku ne, babu wata hanya sahihiya da Gwamnatin Nigeria ta amince da ita domin a canza Gwamnati ko a canza shugabanni da ake ganin sun kasa cika alkawari imba ta hanyar zabe ba
Sanin kan mu ne ana zabe ne da katin zabe na kasa "Permanent Voters Card" (PVC), katin zabe shine makamin da kowani dan Nigeria zai mallaka domin ya canza kowani irin azzalumin shugaba a Nigeria
Yanzu haka ana cigaba da gudanar da rijistan katin zabe, kiyasi ya nuna cewa an bar 'yan Arewa Musulmi a baya, mutanen Kudancin Nigeria sun mana nisa sosai wajen mallakar katin zabe, za'a wayi gari yawan da muke dashi a Arewa ba zai amfana mana da komai ba idan har bamu farga mun mallaki katin zabe ba
Yanzu haka matakin da abokan zaman mu Kiristoci s**a dauka akan mallakar katin zabe shine; sun kai matakin da s**a fara hana mabiyansu shiga cikin Coci ga duk wanda bai mallaki katin zabe ba k**ar yadda jaridar Legit ta ruwaito, abinda Kirista zai nuna a barshi ya shiga cikin Coci shine katin zabe saboda muhimmancinsa
To wannan ya k**ata ya zama babban abin ankararwa garemu Musulmai, ya zama wajibi Sarakunan Arewa, da Manyan Malaman addinin Musulunci na Arewa su fara kira ga Musulmi su je su mallaki katin zabe, da katin zabe zamu canza kowani irin mugun shugaba a Nigeria
Duk Musulmi da yace ba zaiyi zabe ba, ko ba zai mallaki katin zabe ba, to k**ar ya taimaka ne wajen kawo miyagun shugabanni azzalumai wadanda zasu cigaba da take hakkin talakawa, don haka ka cuci kanka, kuma ka cutar da 'yan uwanka Musulmi
Don Alla 'yan uwa a taimaka a yada wannan sanarwan zuwa ga inda ya dace
Muna rokon Allah Ya mana zabi na alheri