Molash Media Connect, Soba Local Government.

Molash Media Connect, Soba Local Government. Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Molash Media Connect, Soba Local Government., Government Organization, Soba.

SOBA TA KARƁI SHIRIN DUBA MARASA LAFIYA DA TIYATA KYAUTA.Al’umma mai lafiya itace ginshiƙin cigaba. A saboda haka, ƙadda...
07/09/2026

SOBA TA KARƁI SHIRIN DUBA MARASA LAFIYA DA TIYATA KYAUTA.

Al’umma mai lafiya itace ginshiƙin cigaba. A saboda haka, ƙaddamar da shirin duba marasa lafiya da yin tiyata kyauta a Ƙaramar Hukumar Soba, babban abin farin ciki ne, musamman ga marasa galihu da waɗanda ke fuskantar ƙalubalen kuɗin samun ingantacciyar kulawar lafiya.

Shirin, wanda Uba Sani Engagement and Sensitization Forum (USESF) ta shirya ƙarƙashin jagorancin Alhaji Adamu Sani, zai taimaka wajen kusantar da kulawar lafiya ga jama’a, tare da ba mutane damar samun magani da tiyatar da suke buƙata ba tare da nauyin kuɗaɗen asibiti ya hana su ba.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Soba, Hon. Muhammad Shehu Molash, ya bayyana matuƙar farin cikinsa da wannan shiri, tare da yabawa jagororin USESF bisa wannan kyakkyawan tunani da sadaukarwar da s**a yi wajen tallafawa al’umma. Ya kuma tabbatar da cikakken goyon bayan gwamnatin ƙaramar hukumar ga duk wani shiri da zai kawo sauƙi da inganta rayuwar jama’a.

Hon. Molash ya kuma miƙa godiya da jinjina ta musamman ga Mai Girma Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, bisa yadda gwamnatinsa ke ƙara faɗaɗa ayyuka da shirye-shirye zuwa ga jama’a a fannoni daban-daban, musamman harkokin kiwon lafiya. Ya bayyana cewa irin wannan himma na nuna ƙudirin gwamnati na tabbatar da jin daɗin al’umma.

Wannan mataki ya sake bayyana irin tsantsar goyon bayan Hon. Muhammad Shehu Molash ga manufofi da tsare-tsaren gwamnatin Sanata Uba Sani, tare da ƙudirin ci gaba da haɗa hannu da gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki domin ganin al’ummar Soba sun ci gaba da amfana da ayyukan cigaba.

Haka kuma, Hon. Molash na cigaba da ƙoƙarinsa wajen ƙarfafa haɗin kan jam’iyya da jagoranci a Soba, tare da yin aiki domin ganin APC ta samu cikakkiyar nasara a dukkan kujerun da take takara a Ƙaramar Hukumar Soba.

7 ga Satumba, 2026

FREE MEDICAL AND SURGICAL OUTREACH LAUNCHED IN SOBA LGA, KADUNA STATE.Soba Local Government Area this morning hosted the...
07/09/2026

FREE MEDICAL AND SURGICAL OUTREACH LAUNCHED IN SOBA LGA, KADUNA STATE.

Soba Local Government Area this morning hosted the official launch of a major Free Medical and Surgical Outreach Programme being implemented across the 23 Local Government Areas of Kaduna State.

The initiative, organised by the Uba Sani Engagement and Sensitization Forum (USESF) under the leadership of its Chairman, Alhaji Adamu Sani, is aimed at bringing essential medical services closer to the people, particularly those who may face difficulties accessing quality and affordable healthcare.

The launch in Soba attracted the presence of several distinguished personalities, including Dr. Mukhtar Ramalan Yero, former Governor of Kaduna State and APC candidate for Kaduna North Senatorial District; Senator Suleiman Hunkuyi, former Senator representing Kaduna North Senatorial District; Dr. Bello Jamo, Secretary of the Kaduna State Primary Health Care Board; alongside numerous other prominent guests, health professionals, political leaders and stakeholders.

The distinguished guests were accorded a warm and special reception by the host, the Executive Chairman of Soba Local Government, Hon. Muhammad Shehu Molash, who expressed his appreciation for the initiative and reaffirmed his administration’s support for programmes that directly improve the welfare of the people.

Speaking on the occasion, Hon. Molash expressed his profound gratitude to His Excellency, Senator Uba Sani, Executive Governor of Kaduna State, for his commitment to improving healthcare delivery across the state and for supporting the launch of this important programme in Soba Local Government Area.

The Executive Chairman noted that bringing free medical consultations, treatments and surgical services directly to communities is a significant step towards ensuring that more residents have access to the healthcare they need, regardless of their financial circumstances.

The launch marks another important milestone in the effort to strengthen healthcare access across Kaduna State, with thousands of residents expected to benefit from the free medical and surgical services as the outreach extends to Local Government Areas across the state.

7th September, 2026

Yau, an gudanar da Kaddamar da Shirin Ba da Agajin Lafiya da Tiyata Kyauta (Free Medical/Surgical Outreach) a Dahiru Mai...
07/09/2026

Yau, an gudanar da Kaddamar da Shirin Ba da Agajin Lafiya da Tiyata Kyauta (Free Medical/Surgical Outreach) a Dahiru Maigana Secretariat, Maigana, cikin nasara. Taron ya samu halartar manyan baki da s**a haɗa da His Excellency, Dr. Mukhtar Ramalan Yero, ɗan takarar Sanata na Shiyyar Kaduna ta 1, Dr. Ihamo, Dr. Bola Ige,

Sanata Suleiman Othman Hunkuyi, Dr. Samaila Suleiman Yakawada, Dr. Halliru Musa Soba, Dr. Jamoh, Executive Secretary na KSPHCB, da sauran manyan jami’an APC Stakeholders, APC Bearer Members, shugabanni da ƙwararrun ma’aikatan lafiya. Hon. Muhammad Shehu Molash, Shugaban Ƙaramar Hukumar Soba, ya tarbi manyan baƙin da kyakkyawar tarba, tare da nuna godiya da maraba da su zuwa Soba.

Wannan shiri ya sake nuna irin kulawa da jajircewar Mai Girma Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Dr. Uba Sani, wajen inganta rayuwar al’umma da samar da damar samun kulawar lafiya. Haka kuma, yana nuna cewa Dr. Uba Sani na da jajirtattun magoya baya da masu kare manufofinsa,

waɗanda suke ƙoƙari dare da rana domin ganin an samu nasara. A yayin shirin, an samu nasarar yi wa mutane 50 tiyata, yayin da wasu da dama s**a samu duba lafiyarsu da magunguna kyauta. Wannan babbar nasara ce ga al’ummar Soba, kuma muna fatan irin wannan tallafi da ayyukan alheri za su ci gaba da ƙara bunƙasa.

7th September, 2026

Aikin sake gina Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Rahama ya kusa kammaluwa a  ƙarƙashin shirin KAD-EDU PAC na gwamnatin ...
04/09/2026

Aikin sake gina Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Rahama ya kusa kammaluwa a ƙarƙashin shirin KAD-EDU PAC na gwamnatin Jihar Kaduna, wanda gwamnatin Gwamna Sanata Uba Sani ta ƙaddamar domin faɗaɗa damar samun ingantaccen ilimi tare da inganta kayayyakin more rayuwa a sashin ilimi a faɗin jihar.

Aikin ya biyo bayan buƙatar da al’ummar Rahama s**a gabatar, inda Shugaban Ƙaramar Hukumar Soba, Hon. Muhammad Shehu Molash, ya taka muhimmiyar rawa wajen ganin an amince da aikin ta hanyar ci gaba da bibiyar buƙatar tare da tuntuɓar hukumomin da abin ya shafa.

Bayan an kammala aikin, ana sa ran makarantar za ta samar da ingantaccen muhalli mai kyau da aminci ga ɗalibai da malamai, tare da ƙara haɓaka damar samun ingantaccen ilimi ga al’ummar Rahama da ƙauyukan da ke makwabtaka da ita.

~ Molash Media Connect
September 4th, 2026

Hon. Muhammad Shehu Molash ba jagora ne kawai ba, shi malami ne na musamman a fannin shugabanci, siyasa da kuma zamantak...
03/09/2026

Hon. Muhammad Shehu Molash ba jagora ne kawai ba, shi malami ne na musamman a fannin shugabanci, siyasa da kuma zamantakewa, wanda ya sadaukar da lokacinsa da ƙarfinsa wajen yiwa al’ummar ƙaramar hukumar Soba hidima, da samar da cigaba mai ma’ana.

Jagorancinsa ya zama abin koyi na hangen nesa, hikima, sadaukarwa da kishin al’umma. Yana koyar da shugabanci ta hanyar aikinsa da kuma kyakkyawan mu'amalarsa da al'umma.

Saboda haka, ya dace mu cigaba da ba Hon. Molash cikakken goyon baya da haɗin kai, domin ya samu damar ci gaba da kawo sabbin manufofi, ayyukan cigaba da kyakkyawar shugabanci ga al’ummar Ƙaramar Hukumar Soba.

Molash Jagora ne !
Kuma abin koyi !

SOBA COUNCIL CHAIRMAN JOINS KADUNA LG CHAIRMEN TO CELEBRATE DEPUTY GOVERNOR HADIZA BALARABE @ 60.The Executive Chairman ...
03/09/2026

SOBA COUNCIL CHAIRMAN JOINS KADUNA LG CHAIRMEN TO CELEBRATE DEPUTY GOVERNOR HADIZA BALARABE @ 60.

The Executive Chairman of Soba Local Government, Hon. Muhammad Shehu Molash, alongside his fellow Local Government Council Chairmen across Kaduna State, joined the Commissioner for Local Government and Chieftaincy Affairs, Hon. Sadiq Mamman Lagos, to celebrate the 60th birthday anniversary of the Deputy Governor of Kaduna State, Her Excellency, Dr. Hadiza Sabuwa Balarabe.

The celebration was organised shortly after the August 2026 Joint Account Allocation Committee (JAAC) plenary meeting, held at the Kaduna State Ministry for Local Government and Chieftaincy Affairs and chaired by the Deputy Governor.

Dr. Hadiza Balarabe, born on 26 August 1966, is a medical doctor, public health specialist and seasoned administrator whose career has been marked by dedicated service to humanity and Kaduna State. She previously served as Director of Public Health in the Federal Capital Territory and later became Executive Secretary of the Kaduna State Primary Health Care Development Agency, where she contributed significantly to strengthening primary healthcare delivery across the state.

In 2019, she made history as the first woman elected Deputy Governor of Kaduna State, and she was re-elected in 2023. Since assuming office, she has continued to play an important role in supporting government policies, coordinating key responsibilities and contributing to the administration’s development agenda.

The Soba Local Government Chairman and his colleagues therefore joined well-wishers in celebrating a remarkable public servant whose experience, commitment and contributions continue to add value to the governance and development of Kaduna State.

Happy 60th Birthday Anniversary, Her Excellency, Dr. Hadiza Sabuwa Balarabe. May Almighty Allah grant you continued good health, wisdom and many more years of impactful service to humanity and Kaduna State.

3rd September, 2026

SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR SOBA YA BI SAHUN SHUGABANNIN KANANAN HUKUMOMIN KADUNA WAJEN TAYA MATAIMAKIYAR GWAMNAN KADUNA, H...
03/09/2026

SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR SOBA YA BI SAHUN SHUGABANNIN KANANAN HUKUMOMIN KADUNA WAJEN TAYA MATAIMAKIYAR GWAMNAN KADUNA, HADIZA BALARABE, MURNAR CIKA SHEKARU 60

Shugaban Ƙaramar Hukumar Soba, Hon. Muhammad Shehu Molash, tare da takwarorinsa Shugabannin Ƙananan Hukumomi a faɗin Jihar Kaduna, sun haɗa kai da Kwamishinan Ƙananan Hukumomi da Harkokin Masarautu, Hon. Sadiq Mamman Lagos, wajen taya Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Mai Girma Dr. Hadiza Sabuwa Balarabe, murnar cika shekaru 60 da haihuwa.

An gudanar da wannan biki ne jim kaɗan bayan kammala taron Kwamitin Kasafi na Asusun Haɗin Gwiwa (JAAC) na watan Agusta 2026, wanda aka gudanar a Ma’aikatar Ƙananan Hukumomi da Harkokin Masarautu ta Jihar Kaduna, ƙarƙashin jagorancin Mataimakiyar Gwamna.

An haifi Dr. Hadiza Balarabe a ranar 26 ga Agusta, 1966. Ita likita ce, ƙwararriya a fannin kiwon lafiyar jama’a, kuma gogaggiyar ma’aikaciyar gwamnati wadda rayuwarta ta kasance mai cike da sadaukarwa wajen yi wa al’umma da Jihar Kaduna hidima.

A baya, ta taɓa riƙe muƙamin Daraktar Kiwon Lafiyar Jama’a a Babban Birnin Tarayya (FCT), sannan daga bisani ta zama Sakatariyar Zartarwa ta Hukumar Bunƙasa Kula da Lafiya ta Matakin Farko ta Jihar Kaduna. A wannan matsayi, ta taka muhimmiyar rawa wajen ƙarfafa da inganta harkokin kiwon lafiya na matakin farko a faɗin jihar.

A shekarar 2019, ta kafa tarihi a matsayin mace ta farko da aka zaɓa a matsayin Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, sannan aka sake zaɓenta a karo na biyu a shekarar 2023.

Tun bayan hawanta kan muƙamin, ta cigaba da taka muhimmiyar rawa wajen tallafawa manufofin gwamnati, gudanar da muhimman ayyuka da kuma bayar da gudunmawa wajen aiwatar da manufofin cigaban gwamnatin Jihar Kaduna.

Saboda haka, Shugaban Ƙaramar Hukumar Soba, tare da takwarorinsa, sun haɗa kai da sauran masu fatan alheri wajen bikin wannan gagarumar hidimar da wata fitacciyar ma’aikaciyar gwamnati ta yi, wadda gogewarta, jajircewarta da gudunmawarta s**a cigaba da ƙarawa harkokin shugabanci da cigaban Jihar Kaduna daraja.

Murnar cika shekaru 60 da haihuwa, Mai Girma Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Dr. Hadiza Sabuwa Balarabe.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki ya cigaba da ba lki lafiya, hikima da basira, tare da tsawaita rayuwarki cikin alheri, domin cigaba da yi wa al’umma da Jihar Kaduna hidima mai amfani.

3 ga Satumba, 2026

SOBA LOCAL GOVERNMENT CHAIRMAN ATTENDS THE AUGUST 2026 JOINT ACCOUNTS ALLOCATION COMMITTEE (JAAC) MEETINGThe Executive C...
02/09/2026

SOBA LOCAL GOVERNMENT CHAIRMAN ATTENDS THE AUGUST 2026 JOINT ACCOUNTS ALLOCATION COMMITTEE (JAAC) MEETING

The Executive Chairman of Soba Local Government, Hon. Muhammad Shehu Molash, joined his fellow Local Government Chairmen at the August 2026 Joint Accounts Allocation Committee (JAAC) Meeting, held today at the Senator Uba Sani Conference Hall, Ministry of Local Government, Kaduna.

The meeting was chaired by the Commissioner for Local Government, Hon. Sadiq Mamman Lagos, as part of the established process for coordinating and facilitating the allocation of funds from the Federation Account to the 23 Local Government Areas of Kaduna State.

The meeting brought together key government officials, including the Permanent Secretary of the Ministry, Dr. Mahmud Lawal; the Senior Special Assistant to the Governor on Local Government, Hon. Usman Lado Dan Daura; the Governor’s Technical Adviser, Hajiya Zarah Askira; the Chairmen of the 23 Local Government Areas; Directors of the Ministry; the Commander of the Kaduna State Vigilante Service; and representatives of key agencies, including SUBEB, the Office of the Accountant-General, the Primary Health Care Board, the Pension Board, and the Local Government Staff Management Board.

The discussions focused on financial coordination, transparency, accountability, and effective management of public resources, with the aim of further improving public welfare services and promoting sustainable development across the Local Government Areas.

Hon. Molash’s participation in such an important meeting further demonstrates his commitment to good governance, accountability, responsible leadership, and sustainable development for the people of Soba Local Government.

2nd September, 2026

SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR SOBA YA HALARCI TARON KWAMITIN  KASAFI NA ASUSUN HAƊIN GWIWA (JAAC MEETING) NA WATAN AGUSTA 202...
02/09/2026

SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR SOBA YA HALARCI TARON KWAMITIN KASAFI NA ASUSUN HAƊIN GWIWA (JAAC MEETING) NA WATAN AGUSTA 2026.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Soba, Hon. Muhammad Shehu Molash, ya bi sahun takwarorinsa shugabannin ƙananan hukumomi wajen halartar taron Kwamitin Kasafi na Asusun Haɗin Gwiwa (JAAC Meeting) na watan Agusta 2026, wanda ya gudana yau a ɗakin taro na Sanata Uba Sani (Senator Uba Sani Conference Hall) dake ma'aikatar ƙananan hukumomi, Kaduna.

Kwamishinan ƙananan hukumomi, Hon. Sadiq Mamman Lagos shine ya jagoranci taron, a matsayin wani ɓangare na tsarin da ake bi wajen daidaita rabon kuɗaɗen Asusun Tarayya ga ƙananan hukumomi 23 na Jihar Kaduna.

Taron ya haɗa manyan jami’an gwamnati, ciki har da Babban Sakataren Ma’aikatar, Dr. Mahmud Lawal; Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamna kan Ƙananan Hukumomi, Hon. Usman Lado Dan Daura; Mai Ba Gwamna Shawara kan Fasaha, Hajiya Zarah Askira; Shugabannin ƙananan hukumomi 23; Daraktocin Ma’aikatar; Kwamandan Kaduna State Vigilante Service, da wakilan muhimman hukumomi kamar SUBEB, Ofishin Akanta-Janar, Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko, Hukumar Fansho, da Hukumar Kula da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi.

Tattaunawar ta mayar da hankali kan daidaita harkokin kuɗi, gaskiya, riƙon amana da ingantaccen tsarin amfani da albarkatun jama’a, domin ƙara inganta ayyukan jin daɗin al’umma da ci gaban ƙananan hukumomi.

Kasancewar Hon. Molash cikin irin wannan muhimmin taro na ƙara nuna jajircewarsa wajen samar da shugabanci nagari, riƙon amana da cigaba mai ɗorewa ga al’ummar Soba.

2nd September, 2026

Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Soba, sannan ɗan takarar Majalisar Dokokin Jihar Kaduna a Gundumar Maigana, a ƙarƙas...
01/09/2026

Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Soba, sannan ɗan takarar Majalisar Dokokin Jihar Kaduna a Gundumar Maigana, a ƙarƙashin tutar Jam’iyyar APC, Hon. Muhammed Garba (Baban-Baba), na miƙa gaisuwar barka da shiga sabon watan Satumba ga al’ummar Gundumar Maigana, Ƙaramar Hukumar Soba da Jihar Kaduna baki ɗaya.

Muna roƙon Allah ya sanya wannan sabon wata ya zo mana da zaman lafiya, cigaba, wadata, albarka da sabbin damammaki. Allah ya jagorance mu, ya kare iyalanmu, ya kuma sanya Satumba ya zama wata mai cike da nasara da alheri ga kowa.

1st September, 2026

Address

Soba

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Molash Media Connect, Soba Local Government. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share