30/04/2026
YANZU-YANZU: Nafi’u Bala Ya Sha Kaye — Kotu Ta Tabbatar da David Mark a matsayin Shugaban ADC
Kotun Ƙoli ta Najeriya ta yanke hukunci mai muhimmanci a rikicin shugabancin jam’iyyar ADC, inda ta tabbatar da bangaren da tsohon shugaban Majalisar Dattawa, David Mark ke jagoranta.
Hukuncin ya zo ne bayan da kotun ta soke umarnin da ya bukaci bangarorin rikicin su ci gaba da zama yadda suke kafin fara shari’a, wanda a baya ya bai wa wasu bangarori damar jingina da shi.
Da wannan mataki, Nafi’u Bala ya sake shan kaye a shari’ar, yayin da shugabancin bangaren David Mark ya samu ƙarfi a idon doka.
Masu sharhi na ganin wannan hukunci zai iya kawo sauyi mai girma a cikin rikicin jam’iyyar, tare da sake fasalin siyasar ADC gaba ɗaya.