17/05/2026
MAHAIFIYAR UMAR ABAR ZARGI CE!!!
A cigaba da Sauraren Shari'ar da ake yi wa su Umar da abaokan ta'addancinsa a bisa tuhumar kashe kashe a Unguwar Tudun Yola da Unguwar Ciranci
Jiya a zaman kotun Mijin ƙanwar Mahaifiyar Umar Wanda s**a kashewa matansa a Unguwar Tudun Yola ya Shaidawa kotu cewa
Bayan kisan da a ka yi wa matarsa kafin a raba gadonta Sai mahaifiyar Umar wacce Yayar mamaciyar ce ta kira Shi ta ce ai Umar ya ba wa ƙanwartata mamaciyar ajiyar kuɗi naira dubu ɗari biyar 500k da ɗan kunnen gwal
Sai mijin ya shiga tunani Saboda bai san da maganar ba matrsa bata sanar da shi ba amma a haka ya ɗauki kuɗin ya biya don a zauna Lafiya
Abin mmaki kuma Sai yanzu Shi Umar ɗin ya Shaidawa Jami'an tsaro da kotu ce wa Sam bai bata ajiyar Kuɗi da Gwal ɗin ba ƙarya yake yi kawai sun shirya haka ne don samun kuɗi
Kuma Shi Umar ɗin ya ce yana daga cikin dalilin da ya sa s**a kasheta har da hana su wannan kuɗin da ɗan kunnen Gwal da ta yi
Anan yakamata Mahaifiyar Umar ta zamo abin Zargi Saboda yadda ta goyi bayansa a kan zalunci da zambar kuɗaɗe da ya Shirya ta kasa banbance tsakanin gaskiya da ƙarya
In Shaa Allah duk Lokacin da gaɓa mai mahimmanci ta baiyana a cikin wannan Shari'ar za a bayyana muku
Allah Ya kyauta Ya Shiga tsakanin nagari da mugu Ya tsare mu damalmalewar wannan zamanin.
Abbas Adamu - 16 - 5 - 2026 -