28/05/2026
ZIYARAR GAISUWA DA BARKA DA ZUWA
Kwamishinan Ilimi Matakin Farko na jihar Yobe, Associate Abba Idris Adam ya kai ziyarar jaje da gaisuwar lafiya ga Malam Musa Kallah bayan dawowarsa daga ƙasar Egypt, inda ya je domin kula da lafiyarsa.
A yayin ziyarar, Kwamishinan ya bayyana farin cikinsa da ganin Malam Musa Kallah cikin ƙoshin lafiya bayan dawowarsa gida lafiya. Yace wannan ziyara ta nuna muhimmancin kula da juna da kuma nuna ƙauna da tausayi tsakanin al’umma, musamman ga waɗanda s**a fuskanci rashin lafiya.
Kwamishinan ya yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki ya ci gaba da ba Malam Musa Kallah cikakkiyar lafiya da nisan kwana, ya kuma kare shi daga dukkan wani rashin lafiya a nan gaba. Haka kuma ya jajanta tare da ƙarfafa masa guiwa kan muhimmancin cigaba da kula da lafiyarsa kamar yadda likitoci s**a ba shi shawara.
Shi ma Malam Musa Kallah ya nuna godiya matuƙa bisa wannan ziyara ta karamci da nuna kulawa da Kwamishinan Ilimi ya kai masa, yana mai cewa irin wannan ziyara na ƙara dankon zumunci.
✍🏿 Muhammad Adamu Malami
P.A to the Honourable Commissioner,
MOBSE YOBE STATE
28052026