22/08/2026
ALH. IBRAHIM KABIR MASARI YA HALARCI TARON MUSULMIN AREWA YAYIN DA S**A NUNA GOYON BAYANSU GA SHUGABA TINUBU A SHEKARAR 2027
A GARIN DUTSEN JIHAR JIGAWA, MALAMAN ISLAMA DA SHUGABANNIN ADDINAI DABAN-DABAN SU DARI BIYAR (500) S**A NUNA GOYON BAYANSU GA SHUGABAN KASA BOLA AHMAD TUNUBU A YAU ASABAR 22ND AUGUST, 2026.
Mai Girma, Alhaji Ibrahim Kabir Masari, Babban Mai Taimakawa Shugaban Kasa a Fannin Siyasa da Alamuran Yau da Kullum, ya halarci Taron Masana da Malaman Addinin Musulnci na Arewa wanda aka gudanar a Hilin Sir Ahmadu Bello, Sabon Sakatariyata, Dutse, Jihar Jigawa, inda malamai da shugabannin addini kusan 500 s**a goyi bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, domin sake zabensa a shekarar 2027 tare da nuna amincewa da tafiyar gwamnatinsa.
Taron ya tara manyan malamai, masana, shugabannin addini da sauran masu ruwa da tsaki da aka gayyata daga jihohi 19 na Arewacin Nijeriya da Babban Birnin Tarayya Abuja (FCT), inda mahalarta taron s**a tattauna kan batutuwan da s**a shafi tsaro, tattalin arziki, da kalubalen ci gaba da s**a shafi yankin.
Daga cikin wadanda s**a halarci taron akwai Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi; Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf; Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni; Gwamnan Jihar Sokoto, Ahmad Aliyu; da Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani.
Haka kuma akwai Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, da Ministan Muhalli da Ci gaban Birane, Dr. Muttaka Rabe Darma.
Taron ya samu halartar shehunan malamai da shugabannin addini kusan 500, ciki har da Manya-manya Shehunai, Limamai, Alaramomi (Malamai Masu Haddar Al-Qur’ani), da Masu Wa’azin Musulunci.
Mahalarta taron sun duba yanayin ci gaban da aka samu a fadin Arewacin Nijeriya, tare da ba da muhimmanci na musamman ga fannin tsaro, abubuwan more rayuwa, da tattalin arziki.
Haka zalika Sun nuna gamsuwarsu da tsarin da Shugaba Tinubu ya dauka wajen tunkarar kalubalen da ke fuskantar Arewa, musamman matsalar rashin tsaro, tare da murna da irin ci gaban da aka samu a karkashin gwamnatinsa.
A matsayar da s**a dauka gaba daya, mahalarta taron sun nuna amincewa da goyon bayansu ga Shugaba Tinubu domin sake zabensa a zaben shugaban kasa na shekarar 2027, inda s**a nuna kwarin gwiwa kan turbar da gwamnatinsa ke kaiwa da kokarinta wajen gyaran tattalin arziki, samar da abubuwan more rayuwa, tsaro, da sake gina kasa.
Haka kuma, taron ya jaddada kwarin gwiwa ga Shugaba Tinubu sannan ya yi kira ga 'yan Nijeriya, musamman mutanen Arewa, da su goyi bayan sake zabensa tare da zaba masa sauran 'yan takarar Jam'iyyar APC a zabuka masu zuwa.
Mahalarta taron sun jaddada muhimmancin haɗin kai, kwanciyar hankali a siyasa, da kyakkyawar alaka tsakanin shugabannin siyasa, na addinai, da na al'umma, inda s**a bayyana cewa dorewar hadin kai shi ne makullin samun nasara wajen karfafa tsaro, bunkasa tattalin arziki, da samar da zaman lafiya a fadin yankin na Arewa.
Taron ya kammala da sabunta aniyarsu ta yin zaman lafiya, hadin kan al'umma, kasancewa 'yan kasa na gari, da goyon bayan dukkan tsare-tsaren da za su ciyar da bukatun Arewacin Nijeriya da kasa baki daya gaba.
Sa hannu:
Ofishin Yada Labarai
Ibrahim Masari Solidarity Organisation (IMSO)