Ibrahim Masari Solidarity Organisation IMSO

Ibrahim Masari Solidarity Organisation IMSO Advancing the Renewed Hope Agenda through the office of H.E. Ibrahim Masari, S.A Political Matters

Mai Ba Shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa, Alhaji Ibrahim Kabir Masari ya shirya tattaunawa Da Manyan Malaman jam...
12/09/2026

Mai Ba Shugaban ƙasa shawara kan harkokin siyasa, Alhaji Ibrahim Kabir Masari ya shirya tattaunawa Da Manyan Malaman jami’o’i Na Arewacin Najeriya Kan Nasarorin Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu (Asiwaju) Da Kuma Makomar Siyasa Zuwa 2027.

Mai Baiwa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Siyasa, Alhaji Ibrahim Kabir Masari Tare Da Rakiyar Shugaban Hukumar AUDA/N...
11/09/2026

Mai Baiwa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Siyasa, Alhaji Ibrahim Kabir Masari Tare Da Rakiyar Shugaban Hukumar AUDA/NEPAD Honarabul Jabiru Salisu Tsauri, Sun Kai Ziyarar Ta'aziyyar Rasuwar Sanata Bello Mandiya A Gidan Sa Dake Malumfashi, Jihar Katsina Yau Juma'ah 11th Sept, 2026.

Building the Grassroots, & Securing the Feature.  Let's cast our Vote here.
10/09/2026

Building the Grassroots, & Securing the Feature. Let's cast our Vote here.

MEDIA TEAM!!!
07/09/2026

MEDIA TEAM!!!

Mai Girma, Alhaji Ibrahim Kabir Masari, Babban Mai Taimakawa Shugaban Kasa ta fannin Siyasa  da Alamuran Yau da Kullum, ...
04/09/2026

Mai Girma, Alhaji Ibrahim Kabir Masari, Babban Mai Taimakawa Shugaban Kasa ta fannin Siyasa da Alamuran Yau da Kullum, ya kai ziyarar jaje ga iyalai da kaddarar matsalar 'yan bindiga ta shafa al'ummar Gidan Lumu da ke Karamar Hukumar Kafur a Jihar Katsina.

​A yayin ziyarar, Ibrahim Masari ya mika sakon ta'aziyyarsa ga iyalan Alhaji Samaila Sarkin Noma bisa rasuwar Saifullahi Gambo, wanda ya rasa ransa a wani hari da 'yan bindiga s**a kai. Ya yi addu'ar Allah ya jikansa da rahama, tare da bayar da kalamai na karfafa gwiwa ga iyalan mamacin.

​Haka zalika, ya nuna jajensa da alhininsa ga iyalan yaran da 'yan bindiga s**a sace, inda ya bayyana damuwarsa da goyon bayansa gare su, tare da yin addu'ar Allah ya kubutar da yaran cikin aminci da salama.

​Alhaji Maiwada Daudawa shima ya gudanar da addu'o'i ga mamacin da iyalan da abin ya shafa.

​Wannan ziyara ta sake jaddada matsayar Ibrahim Masari ta kasancewa tare da mutanen da matsalar rashin tsaro ta shafa, gami da nuna damuwarsa kan tsaro da jin dadin al'ummomin fadin Jihar Katsina.
​Babban Mai Taimakawa Shugaban Kasan ya samu rakiyar Mai Girma Ministan Muhallayi da Ci gaban Birane, Dr. Muttaka Rabe Darma; Babban Darekta Janar na Hukumar Kula da Ilimin Almajirai da Yaran da Ba Su Zuwa Makanta ta Kasa, Dr. Muhammad Idris; Hon. Jabiru Tsauri; Alhaji Maiwada Daudawa; Dr. Shehu Matazu; Hon. Aminu Ibrahim Kafur; da Hon. Samaila Garba Sabuwar Kasa.

​Sa hannu:
Ofishin Yada Labarai,
Ibrahim Masari Solidarity Organisation (IMSO)

03/09/2026
*ALHAJI IBRAHIM KABIR MASARI: THE POLITICAL ENGINE THAT WILL DELIVER MASSIVE VOTES FOR PRESIDENT TINUBU IN 2027*In polit...
31/08/2026

*ALHAJI IBRAHIM KABIR MASARI: THE POLITICAL ENGINE THAT WILL DELIVER MASSIVE VOTES FOR PRESIDENT TINUBU IN 2027*

In politics, results speak louder than noise. And as we approach the *2027 General Election*, one name stands tall as the bridge between *President Bola Ahmed Tinubu* and the grassroots of Northern Nigeria — *Alhaji Ibrahim Kabir Masari*, the *Senior Special Assistant to the President on Political Matters*.

*THE STRATEGIST BEHIND THE SCENES*
Appointed at a defining moment, Alhaji Masari was not given an office just to sit. He was given a mandate: *Mobilize, Unite, and Deliver*.
Today, he has become the most trusted political link between the Presidency and the 19 Northern States. From Sokoto to Borno, from Kano to Niger, his voice resonates in palaces, party meetings, and village squares.

*WHY HE IS THE ONE TO DELIVER 2027*
1. *Grassroots Connection*
Alhaji Masari does not do politics from Abuja alone. He is on the ground. He knows the Ward Chairmen by name, the Youth Leaders by face, and the community problems by heart. "No community is too far, no vote is too small" is his creed.

2. *Party Cohesion and Mobilization*
He has worked tirelessly to strengthen APC structures across the North. Through town halls, stakeholder meetings, and conflict resolution, he has healed divisions and rebuilt confidence in the Renewed Hope Agenda.

3. *Understanding Northern Dynamics*
As a son of the soil, he understands the pulse of the North — its culture, religion, and expectations. He translates federal policies into local language so that the farmer in Katsina, the trader in Kano, and the student in Maiduguri all feel carried along.

4. *Track Record of Delivery*
Politics is about votes. And Alhaji Masari has shown capacity to organize, mobilize, and turn out voters in large numbers. His network cuts across traditional rulers, religious leaders, women groups, and youth organizations — the real determinants of election outcomes.

*THE 2027 FACTOR*
Come 2027, the North will decide the direction of Nigeria. And to win massively in the North, the President needs a man who is trusted, accessible, and results-driven.
That man is *Alhaji Ibrahim Kabir Masari*.

He is not just an aide. He is *the mobilizer, the unifier, and the vote-getter* that will ensure President Bola Ahmed Tinubu records his biggest victory yet.

*CONCLUSION*
Leadership is about service, loyalty, and results. Alhaji Ibrahim Kabir Masari embodies all three.
With him on the team, the Renewed Hope Agenda will not only be preached — it will be delivered at the ballot box.

*“Service to the People. Loyalty to the President. Victory for Nigeria in 2027.”*

---

Signed.
Prof Armayau Hamisu Bichi.
S.A to the Deputy President of the Senate.
Former VC Federal University Dutsinmaa katsina state.

ALHAJI IBRAHIM KABIR MASARI YA SHUGABANCI TARON NEMAN ILIMI NA KASA A JOS, JIHAR PLATEAU — 23rd AUGUST, 2026​Mai Girma, ...
24/08/2026

ALHAJI IBRAHIM KABIR MASARI YA SHUGABANCI TARON NEMAN ILIMI NA KASA A JOS, JIHAR PLATEAU — 23rd AUGUST, 2026

​Mai Girma, Alhaji Ibrahim Kabir Masari, Babban Mai Taimakawa Shugaban Kasa a kan Alamuran Siyasa da na Yau da Kullum, ya shugabanci taron manema ilimi na kasa na yini guda a kan "Karfafa Shiga Siyasa da Adalci a Tsakanin Al'umma" wanda kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS) ta shirya a garin Jos, Jihar Plateau.

​Taron ya tara Gwamnonin Jihohin Yobe, Jigawa, Kano da Sokoto, tare da Mai Girma Ministan Muhalli da Ci gaban Birane, Dr. Muttaka Rabe Darma, Sheikh Sani Yahaya Jingir, malamai, shugabannin siyasa, jami'an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki domin tattaunawa kan shiga harkar siyasa, adalci a tsakanin al'umma, da ci gaban kasa baki daya.

​A jawabin da ya gabatar a matsayinsa na Shugaban Taron, Alhaji Ibrahim Kabir Masari ya mika godiyarsa ga Sheikh Sani Yahaya Jingir bisa goyon bayan da yake bawa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, tun lokacin zaben shugaban kasa na shekarar 2023 da kuma bayan zaben. Ya yaba da dorewar kyakkyawar alaka da goyon bayan da Shehin Malamin yake bawa gwamnatin.

​Alhaji Ibrahim Kabir Masari ya tabbatar wa taron cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu mutumin kirki ne mai kyakkyawar aniya ga Nijeriya da al'ummarta. Ya kuma yi kira da a ci gaba da yi wa gwamnatin addu'a, ba baata kyakkyawar shawara, da kyakkyawan goyon baya.

​A nasa jawabin, Sheikh Sani Yahaya Jingir ya sake jaddada goyon bayansa ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamnatinsa, gami da tsarin tikitin musulmi da musulmi, tare da daukar alkawarin ci gaba da goyon bayan jagorancin Shugaban Kasan.

​Da yake jawabi a madadin gwamnoni da s**a halarci taron, Mai Girma Mai Mala Buni, Gwamnan Jihar Yobe, ya jaddada muhimmancin shiga siyasa ta hanyar da ta dace, samar da adalci ga al'umma, da haɗin kan kasa.

​Sa hannu:
Ofishin Yada Labarai
Ibrahim Masari Solidarity Organisation (IMSO)
23 ga Abubakar, 2026

ALH. IBRAHIM KABIR MASARI YA HALARCI TARON MUSULMIN AREWA YAYIN DA S**A NUNA GOYON BAYANSU GA SHUGABA TINUBU A SHEKARAR ...
22/08/2026

ALH. IBRAHIM KABIR MASARI YA HALARCI TARON MUSULMIN AREWA YAYIN DA S**A NUNA GOYON BAYANSU GA SHUGABA TINUBU A SHEKARAR 2027

A​ GARIN DUTSEN JIHAR JIGAWA, MALAMAN ISLAMA DA SHUGABANNIN ADDINAI DABAN-DABAN SU DARI BIYAR (500) S**A NUNA GOYON BAYANSU GA SHUGABAN KASA BOLA AHMAD TUNUBU A YAU ASABAR 22ND AUGUST, 2026.

​Mai Girma, Alhaji Ibrahim Kabir Masari, Babban Mai Taimakawa Shugaban Kasa a Fannin Siyasa da Alamuran Yau da Kullum, ya halarci Taron Masana da Malaman Addinin Musulnci na Arewa wanda aka gudanar a Hilin Sir Ahmadu Bello, Sabon Sakatariyata, Dutse, Jihar Jigawa, inda malamai da shugabannin addini kusan 500 s**a goyi bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, domin sake zabensa a shekarar 2027 tare da nuna amincewa da tafiyar gwamnatinsa.

​Taron ya tara manyan malamai, masana, shugabannin addini da sauran masu ruwa da tsaki da aka gayyata daga jihohi 19 na Arewacin Nijeriya da Babban Birnin Tarayya Abuja (FCT), inda mahalarta taron s**a tattauna kan batutuwan da s**a shafi tsaro, tattalin arziki, da kalubalen ci gaba da s**a shafi yankin.

​Daga cikin wadanda s**a halarci taron akwai Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi; Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf; Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni; Gwamnan Jihar Sokoto, Ahmad Aliyu; da Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani.
Haka kuma akwai Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, da Ministan Muhalli da Ci gaban Birane, Dr. Muttaka Rabe Darma.

​Taron ya samu halartar shehunan malamai da shugabannin addini kusan 500, ciki har da Manya-manya Shehunai, Limamai, Alaramomi (Malamai Masu Haddar Al-Qur’ani), da Masu Wa’azin Musulunci.

​Mahalarta taron sun duba yanayin ci gaban da aka samu a fadin Arewacin Nijeriya, tare da ba da muhimmanci na musamman ga fannin tsaro, abubuwan more rayuwa, da tattalin arziki.

Haka zalika Sun nuna gamsuwarsu da tsarin da Shugaba Tinubu ya dauka wajen tunkarar kalubalen da ke fuskantar Arewa, musamman matsalar rashin tsaro, tare da murna da irin ci gaban da aka samu a karkashin gwamnatinsa.

​A matsayar da s**a dauka gaba daya, mahalarta taron sun nuna amincewa da goyon bayansu ga Shugaba Tinubu domin sake zabensa a zaben shugaban kasa na shekarar 2027, inda s**a nuna kwarin gwiwa kan turbar da gwamnatinsa ke kaiwa da kokarinta wajen gyaran tattalin arziki, samar da abubuwan more rayuwa, tsaro, da sake gina kasa.
​Haka kuma, taron ya jaddada kwarin gwiwa ga Shugaba Tinubu sannan ya yi kira ga 'yan Nijeriya, musamman mutanen Arewa, da su goyi bayan sake zabensa tare da zaba masa sauran 'yan takarar Jam'iyyar APC a zabuka masu zuwa.

​Mahalarta taron sun jaddada muhimmancin haɗin kai, kwanciyar hankali a siyasa, da kyakkyawar alaka tsakanin shugabannin siyasa, na addinai, da na al'umma, inda s**a bayyana cewa dorewar hadin kai shi ne makullin samun nasara wajen karfafa tsaro, bunkasa tattalin arziki, da samar da zaman lafiya a fadin yankin na Arewa.

​Taron ya kammala da sabunta aniyarsu ta yin zaman lafiya, hadin kan al'umma, kasancewa 'yan kasa na gari, da goyon bayan dukkan tsare-tsaren da za su ciyar da bukatun Arewacin Nijeriya da kasa baki daya gaba.

​Sa hannu:
Ofishin Yada Labarai
Ibrahim Masari Solidarity Organisation (IMSO)

Address

No:2&3 Nanaco Plaza, 001 Gidan Dawa, Commercial Layout
Katsina
820101

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ibrahim Masari Solidarity Organisation IMSO posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share