28/07/2026
Gamayyar ƙungiyoyin matasa masu goyon bayan shugaba Tinubu tare da haɗin gwiwa da gidauniyar Katsina Healthcare sun gudanar da gangami bada magani da duba lafiya kyauta
A wani yunƙurin haɗin gwiwa da s**ayi domin taimakawa al'umma marassa ƙarfi sun duba marassa lafiya tare da basu magani, da kuma yin awo ga marassa lafiya
An gudanar da gangamin a asibiti Maryam health Care Clinic dake dake Modoji Katsina a ranar 27 ga watan Yuli 2026
A yayin da yake jawabi yayin bada tallafin lafiyar Sakataren tsatsare na ƙungiyar Muhammad Dikko Musa yake cewa wannan haɗin gwiwa ne, tsakanin ƙungyarmu da da wanan asibiti Maryam Clinic domin taimawa marassalafiya wanda basuda halin zuwa asibiti
Ya ƙara da cewa ita kungiyar gamayyar ƙungiyoyin matasa masu goyon bayan Tinubu Coalition Of Youths Organizations For Tinubu/Dikko ba kwai wayar ta kan al'umma kan Shugaba Tunubu ta tsaya kaɗai ba, harda taimako ga al'umma ta fannoni daban-daban
Shima anasa Jawabin shugaban Asibitin ta Maryam Nurse home Katsina Malam Nuhu Idris yace a wanan hadin gwiwa muyi yarjejeniya da ƙungiyar inda muka yafe kaso 15% su kuma s**a bada koso 75% tunda ganin likita, bada magani da kuma aune-aune
Haka zalika muna son yin amfani da wannan dama domin muyi kira ga sauran kungiyoyi da ɗaiɗaikun al'umma da Gwamnati da suyi koyi da wanan ƙungiya sanan kuma a matakin asibitin mu a shirye muke domin tallafawa al'umma musamman ta bangaren lafiya sanan kuma muna rage kaso mai tsoka.
Daga Karshe dai Shugaban kungiyan a yayin jawabin sa yace ita wannan kungiyan a shirye take domin hadin gwiwa da cigaban alumman kasa baki daya