Hon. Engr. Ibrahim Isah Namakka for state House of Assembly Safana LGA

  • Home
  • Nigeria
  • Katsina
  • Hon. Engr. Ibrahim Isah Namakka for state House of Assembly Safana LGA

Hon. Engr. Ibrahim Isah Namakka for state House of Assembly Safana LGA Together we can achieve more for Safana local Government

OUR COMMUNITY FIRST Mun ɗauki Siyasa hanya ta jagorantar al’umma, wakiltar muradunsu, kare haƙƙoƙinsu da neman mafita ga...
03/09/2026

OUR COMMUNITY FIRST
Mun ɗauki Siyasa hanya ta jagorantar al’umma, wakiltar muradunsu, kare haƙƙoƙinsu da neman mafita ga matsalolin da suke fuskanta.

A karkashin jagorancin Hon Engr Ibrahim Isah Namakka ɗan takarar Majalisar Dokokin Jihar Katsina mai wakiltar karamar hukumar safana a jam'iyar PDP POWER TO THE PEOPLE.

A tafiyar siyasar mu zamu kasance masu kamanta gaskiya, adalci, tawali’u, sauraron jama’a, haƙurin da jurewa kalubalantar abokan hamayya da masu s**a. Kuma zamuyi kokarin ganin bambancin ra’ayi bai zama dalilin ƙiyayya, zagi cinmutunci ko tashin hankali tsakanin mu da kowa ba. Insha Allahu.

COMRADE
Yusuf Usman Babban Duhu

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UNA madadin masoya da magoya bayan Hon. Engr. Ibrahim Isah Namakka, da kuma ni kaina, m...
28/08/2026

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN
A madadin masoya da magoya bayan Hon. Engr. Ibrahim Isah Namakka, da kuma ni kaina, muna miƙa saƙon ta’aziyyarmu bisa rasuwar BISHIR YAKUBU BABBAN_DUHU, ga iyalansa, ‘yan uwansa, abokan arziki da daukacin al’ummar garin Babban_Duhu.

Marigayi Bishir Yakubu Babban_Duhu ya kasance surukin Hon. Namakka, wato mahaifin matar sa, wanda ya kasance uba gare mu a Babban_duhu.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya jiƙan marigayin da rahama, Ya gafarta masa kurakurensa, Ya haskaka kabarinsa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ce makomarsa.

Haka kuma muna roƙon Allah Ya ba iyalansa da ‘yan uwansa, musamman Hon. Namakka da iyalansa, da kuma daukacin al’ummar Babban_Duhu, haƙurin jure wannan babban rashi.

Allah Ya albarkaci zuriyar da ya bari, Ya sanya su zama masu amfani ga al’umma, Ya kuma maye musu wannan rashi da mafificin alheri.

Allah Ya jiƙansa da rahama, Ya gafarta masa, Ya sa Aljannatul Firdausi ce makomarsa. Amin.

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN.

Write ✍️
Comrade
Yusuf Usman Babban Duhu

SIYASAR NEMAN KAWO SAUYI GA RAYUWAR AL'UMMA:Hon. Engr. Ibrahim Isah Namakka ya ɗauki siyasa a matsayin wata hanya ta hid...
27/08/2026

SIYASAR NEMAN KAWO SAUYI GA RAYUWAR AL'UMMA:

Hon. Engr. Ibrahim Isah Namakka ya ɗauki siyasa a matsayin wata hanya ta hidimtawa al’umma da kawo sauyi, ba wai wata hanya ta biyan buƙatun kansa kawai ba.

Manufarsa ita ce ganin al’ummar Ƙaramar Hukumar Safana ta samu ci gaba mai ma’ana, ta fuskar ilimi, lafiya, ruwa, hanyoyi, aikin yi, ƙarfafa matasa da sauran abubuwan da s**a shafi rayuwar jama’a.

Siyasar Hon. Namakka siyasa ce da ta ginu bisa gaskiya, kishin al’umma da son ganin sauyi. Ba ya kallon shugabanci a matsayin gata, sai dai a matsayin amana da nauyin da ya rataya a wuyansa na yi wa al’umma hidima.

Saboda haka, idan muka ce siyasa ta gaskiya ce, ya kamata a gan ta cikin manufa, aiki da tasirin da take yi a rayuwar jama’a.

Hon. Engr. Ibrahim Isah Namakka — siyasar gaskiya, siyasar sauyi, siyasar ci gaban Safana.

NAMAKKA CHARITY FOUNDATION: TALLAFIN RUWA GA AL’UMMAR GARIN SAFANA:A cikin ci gaba da ƙoƙarinsa na tallafawa al’umma da ...
23/08/2026

NAMAKKA CHARITY FOUNDATION: TALLAFIN RUWA GA AL’UMMAR GARIN SAFANA:

A cikin ci gaba da ƙoƙarinsa na tallafawa al’umma da taimakawa wajen magance matsalolin da suke addabar jama’a, Hon. Engr. Ibrahim Isah Namakka, ɗan takarar Majalisar Dokokin Jihar Katsina mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Safana a ƙarƙashin tutar Jam’iyyar PDP, ya sake nuna kulawarsa ga jin daɗin al’ummar Safana.

A wannan karon, Hon. Namakka ya bayar da gudummawar kuɗi domin gyaran fanfo da samar da ruwan sha a cikin garin Safana, domin taimakawa al’umma wajen samun ruwa mai tsafta da sauƙaƙa musu wahalar neman ruwan sha.

Ruwa shi ne ginshiƙin rayuwa, kuma samun tsaftataccen ruwan sha na daga cikin muhimman buƙatun kowane al’umma. Saboda haka, wannan tallafi ba wai taimakon gyaran fanfo kawai ba ne, illa gudummawa ce wajen kare lafiyar jama’a da inganta rayuwarsu.

Wannan mataki ya sake nuna irin muhimmancin da Hon. Namakka ke bai wa buƙatun al’umma, musamman abubuwan da s**a shafi ruwa, ilimi, lafiya da jin daɗin jama’a.

Muna roƙon Allah Ya saka masa da mafificin alheri, Ya ƙara masa ikon ci gaba da tallafawa al’umma, Ya buɗe masa ƙofofin nasara, kuma Ya ba shi ikon yi wa al’ummar Ƙaramar Hukumar Safana wakilci na gari.

NAMAKKA CHARITY FOUNDATION — Tallafa wa Al’umma, Gina Makoma Mai Kyau.

Write ✍️
Yusuf Usman Babban Duhu

NAMAKKA CHARITY FOUNDATION:A kokarin da yake yi na tallafawa al’umma da bunƙasa harkar ilimi, Hon. Engr. Ibrahim Isah Na...
23/08/2026

NAMAKKA CHARITY FOUNDATION:
A kokarin da yake yi na tallafawa al’umma da bunƙasa harkar ilimi, Hon. Engr. Ibrahim Isah Namakka, ɗan takarar Majalisar Dokokin Jihar Katsina mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Safana a ƙarƙashin tutar Jam’iyyar PDP, ya sake nuna jajircewarsa wajen ganin ɗalibai sun samu damar ci gaba da karatunsu.

A yayin da aka samu matsalar kuɗaɗen da ake buƙata wanda ta kusa hana ɗaliban GDSS Babban Duhu damar ci gaba da jarabawar SSCE, cikin ikon Allah Hon. Namakka ya samu labarin wannan matsala. Ba tare da ɓata lokaci ba, ya ɗauki matakin tallafawa makarantar da abin da ake buƙata domin ganin ɗaliban sun samu damar gudanar da jarabawarsu.

GDSS Babban Duhu makaranta ce mai daɗaɗɗen tarihi wajen bayar da ilimi da fitar da ƙwararrun ɗalibai. Ta taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa ilimin al’ummar wannan yanki, ba wai ta Ƙaramar Hukumar Safana kaɗai ba, domin ɗalibai daga wasu yankuna ma suna halartar makarantar domin samun ingantaccen ilimi.

Wannan mataki na Hon. Namakka ya sake tabbatar da cewa tallafawa ilimi da taimakon al’umma na daga cikin abubuwan da yake ba muhimmanci. Domin idan aka tallafa wa ilimi, an tallafa wa makomar al’umma ne.

Muna addu’ar Allah Ya saka wa Hon. Engr. Ibrahim Isah Namakka for state House of Assembly Safana LGA da mafificin alheri, Ya ƙara masa ikon tallafawa al’umma, Ya buɗe masa ƙofofin nasara, sannan Ya ba shi ikon wakiltar al’ummar Ƙaramar Hukumar Safana a Majalisar Dokokin Jihar Katsina.

NAMAKKA CHARITY FOUNDATION — Tallafa wa Al’umma, Gina Makoma mai kyau.

Write ✍️
Yusuf Usman Babban Duhu

Ina kuke ne yan amana.
19/08/2026

Ina kuke ne yan amana.

19/08/2026

Matashi, kada ka raina kanka tafiyarka taka ce, kuma lokacinka zai zo. Ka yi hakuri, ka ci gaba da kokari, ka dogara ga Allah.

Mu tashi, mu farka, ’yan Safana! Mun san cewa barci aikin dare ne. Ana son a tsoratar da mu, ana kuma tsoron manyan muta...
19/08/2026

Mu tashi, mu farka, ’yan Safana! Mun san cewa barci aikin dare ne. Ana son a tsoratar da mu, ana kuma tsoron manyan mutanen Safana. Mu yi niyya tun kafin manyan Safana su wuce, domin wallahi, su hakikanin masoyan talakawa ne.

17/08/2026

Da farko sun zaci wasa muke Saida s**aga zahiri kuma hankalin su ya tashi.

Address

Safana Local Government
Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hon. Engr. Ibrahim Isah Namakka for state House of Assembly Safana LGA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share