APC Social Media Organisation Katsina State

APC Social Media Organisation Katsina State All Progress Congresses

HOTUNAGwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda ya kai ziyarar dubiya a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ummaru Musa dak...
12/06/2026

HOTUNA

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda ya kai ziyarar dubiya a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ummaru Musa dake Katsina (FMC) don duba marasa lafiya dake kwance a asibitin.

A yayin ziyarar gwamnan ya gana da marasa lafiya ya kuma tallafawa wasu masu bukata.

Allah ya bamu lafiya da zama lafiya.

Gwamna Radda ya Kaddamar da Cibiyar Habaka Zaman Lafiya da Kare Muhalli a JibiaGwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru ...
11/06/2026

Gwamna Radda ya Kaddamar da Cibiyar Habaka Zaman Lafiya da Kare Muhalli a Jibia

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya kaddamar da Cibiyar habaka Zaman Lafiya ta Sauyin Yanayi (Climate Peace Hub) a Karamar Hukumar Jibiya, wadda sashen cigaba na Majalisar Dinkin Duniya (UNDP) tare da tallafin Ma’aikatar Harkokin Wajen Jamus s**a samar domin magance rikice-rikicen da sauyin yanayi ke haifarwa, inganta juriyar al’umma da kuma bunkasa hanyoyin samun ingantaccen abin dogaro da kai.

Da yake jawabi a wajen taron kaddamarwar, Gwamna Radda ya bayyana cibiyar a matsayin wani muhimmin tsari da zai taimaka wajen magance kalubalen tsaro da ci gaba da sauyin yanayi ke haddasawa. Ya bayyana cewa karuwar takaddama kan filaye, hanyoyin kiwo da albarkatun ruwa na daga cikin abubuwan da s**a haddasa rikice-rikice da kaura a yankin, yana mai jaddada bukatar samar da hanyoyin warware matsalolin da s**a hada da kare muhalli da tabbatar da zaman lafiya.

Cibiyar za ta kasance wata muhimmiyar kafa da za ta samar da bayanan yanayi, sasanta rikice-rikice ta hanyar tattaunawa, bunkasa noma daki zai iya jure sauyin yanayi, inganta tafiyar da albarkatun kasa cikin adalci, da kuma tallafa wa kirkire-kirkire da koyar da sana’o’i ga al’umma. Shirin na daga cikin wani yunkuri na yanki da ya shafi jihohin Katsina da Sokoto, tare da alakarsu da Zamfara da wasu yankuna a Jamhuriyar Nijar.

Gwamna Radda ya yaba wa UNDP da sauran abokan ci gaba bisa goyon bayan da suke bai wa jihar wajen inganta zaman lafiya da dorewar ci gaba. Ya kuma jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su magance kalubalen muhalli da tsaro ta hanyar hadin gwiwa da dabaru.

Kaddamar da wannan Cibiya wani muhimmin mataki ne na inganta zaman lafiya, gina juriyar al’umma da tabbatar da ci gaba mai dorewa ga al’ummomin da sauyin yanayi ke yi wa barazana a fadin Jihar Katsina.

MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government

June 11, 2026.

Gwamna Dikko Radda ya Kaddamar da Gidaje 152 na Yan Gudun Hijira a JibiaGwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ...
11/06/2026

Gwamna Dikko Radda ya Kaddamar da Gidaje 152 na Yan Gudun Hijira a Jibia

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, ya kaddamar da gidaje 152 da wasu muhimman ayyukan inganta rayuwar alumma a Karamar Hukumar Jibiya, a wani kokarin gwamnatinsa na sake farfado da yankunan da matsalar tsaro ta shafa da kuma samar da hanyoyin samun abinci da kudin shiga, tare da tabbatar da zaman lafiya mai dorewa.

An aiwatar da wadannan ayyuka ne ta hanyar hadin gwiwa tsakanin Gwamnatin Jihar Katsina, Sashen Cigaba na Majalisar Dinkin Duniya (UNDP), Gwamnatin Tarayyar Jamus ta hannun GIZ, Gwamnatin Kasar Norway da sauran abokan cigaba daga fadin duniya. Ayyukan sun hada da Cibiyar Zaman Lafiya (Climate Peace Hub) da Koyar da Sana’o’i, samar da wutar lantarki mai amfani da hasken rana ga al’ummar Daddara, gina asibitin dabbobi, gine-ginen a cikin kasuwa, tallafin noma, tallafin kasuwanci, horas da ma’aikata, samar da ruwan sha da fitilun tituna duk a cikin karamar hukumar Jibia.

A jawabinsa na maraba, Shugaban Karamar Hukumar Jibiya, Alhaji Surajo Ado Jibiya, ya yaba wa Gwamna Radda da abokan cigaban bisa kawo wadannan ayyuka da zai inganta rayuwar al’umma tare da bunkasa tattalin arzikin yankin.

A nasa jawabin bude taro, Kwamishinan Harkokin Karkara da Raya Al’umma, Farfesa Abdulhamid Ahmed Mani, ya bayyana ayyukan a matsayin wani babban ci gaba a kokarin samar da zaman lafiya da ci gaban al’umma a jihar. Ya ce shirin ya yi duba ne ga muhimman kalubalen da s**a shafi rashin matsuguni, rashin aikin yi, hanyoyin samun abin dogaro da kuma gina al’umma.

Da take jawabi, Wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya mai kula da Sashen Cigaba (UNDP) a Najeriya, Misis Elsie G. Attafuah, ta yaba wa Gwamnatin Jihar Katsina bisa jajircewarta wajen samar da zaman lafiya da ci gaba mai anfani ga kowa. Ta jaddada cewa dorewar zaman lafiya na bukatar saka hannun jari a rayuwar jama’a, cibiyoyi don habaka tattalin arziki.

A sakonnin fatan alheri da s**a gabatar, Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Dakta Nasiru Mu’azu Danmusa, Jakadiyar Tarayyar Jamus a Najeriya, Mai Girma Annette Günther, da Jakadan Masarautar Norway a Najeriya, Mai Girma Svein Baera, sun yaba da tsarin hadin gwiwar da ake amfani da shi wajen magance matsalolin tsaro da karfafa juriyar al’umma. Sun kuma sake tabbatar da goyon bayansu ga shirye-shiryen da ke inganta zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba mai dorewa a Katsina da yankin Arewa Maso Yamman Nigeria.

A babban jawabinsa, Gwamna Radda ya bayyana gidajen da aka kaddamar a matsayin wata alama ta kokarin dawo da mutunci da martaba ga iyalan da matsalar tsaro ta shafa. Ya bayyana cewa Gwamnatin Jihar Katsina ta samar da filin ginin, katanga, hanyoyin shiga, magudanan ruwa, wajen ibada, makaranta, kayan daki, gudumuwar Naira dubu dari biyu (N200,000) ga kowane magidanci don jan jari da sauran muhimman abubuwan more rayuwa domin cika wannan aiki.

Gwamnan ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar ta bayar da tallafin Naira miliyan 500 ga mutane 500 daga Karamar Hukumar Jibiya ta hannun Hukumar Kula da Ci gaban Sana’o’i da Kasuwanci ta Jihar Katsina (KASEDA), domin taimaka musu wajen farfado da kasuwancinsu da hanyoyin samun kudin shiga.

Yayin da ya sake jaddada cewa tsaro shi ne ginshikin manufar gwamnatinsa ta “Gina Makomarku” (Building Your Future Agenda) , Gwamna Radda ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta zuba sama da Naira biliyan 7 wajen samar da kayan aiki da tallafawa ayyukan tsaro. Ya ce ingantuwar tsaro ta bai wa manoma damar komawa gonakinsu, ta sa kasuwanci ya farfado, tare da dawo da kwarin gwiwa ga al’umma.

Har ila yau, ya yi kira ga hukumomi, abokan cigaba, sarakunan gargajiya da al’umma da su kara hada kai wajen magance tushen matsalolin tsaro domin tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a fadin jihar.

A jawabinsa na godiya, Hakimin Daddara, Alhaji Usman Usman Nagogo, ya gode wa Gwamna Radda, abokan cigaba da dukkan masu ruwa da tsaki bisa wannan gagarumin aiki, tare da tabbatar da cewa al’ummar yankin za su kula da wadannan kayayyakin more rayuwa domin amfanin al’umma da al’ummomin da za su zo nan gaba.

An kammala taron ne da kaddamarwa tare da zagayen duba ayyukan da Gwamna Radda, jakadun kasashen waje, abokan cigaba, sarakunan gargajiya da sauran manyan baki s**a gudanar.

Taron ya samu halartar manyan baki ciki hadda mataimakin gwamnan jihar Katsina, Malam Faruk Lawal Jobe, kakakin majalisar dokokin jihar Katsina, Rt. Hon Nasir Yahya Daura, jakadu daga majalisar dinkin duniya, jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki.

MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government

June 11, 2026.

Gwamna Radda ya nada babban mataimakinsa na musamman kan sauyin yanayi, Malam Suleiman S Ribadu a matsayin Katsina State...
11/06/2026

Gwamna Radda ya nada babban mataimakinsa na musamman kan sauyin yanayi, Malam Suleiman S Ribadu a matsayin Katsina State Focal Person na shirin rangadin wayar dakai akan sauyin yanayi da zai gudana a Nigeria.

HOTUNAYadda gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, Ph.D, ya dawo gida Nigeria bayan kammala aikin hajji a kasa ...
10/06/2026

HOTUNA

Yadda gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, Ph.D, ya dawo gida Nigeria bayan kammala aikin hajji a kasa mai tsarki.

Ya samu tarbar mataimakin gwamna, Malam Faruk Lawal Jobe da wasu daga cikin jami’an gwamnati.

Za’a daura daga inda aka tsaya wajen aikace-aikace don cigaban jihar Katsina.

MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government

June 10, 2026.

A ci gaba da zawarcin jagoran adawar Jihar Katsina, watau tsohon sakataren Gwamnatin Jihar Katsina Dr. Mustapha Muhammed...
09/06/2026

A ci gaba da zawarcin jagoran adawar Jihar Katsina, watau tsohon sakataren Gwamnatin Jihar Katsina Dr. Mustapha Muhammed Inuwa domin ya dawo cikin tsohuwar Jam'iyyarsa ta Apc.

A cikin daren nan na Litinin 8/6/2026, lamba 2 na Jihar Katsina, watau mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Hon. Faruk Lawal Jobe ya ziyarci jagoran adawar a gidan sa dake cikin garin Katsina.

Yayin ziyarar, mataimakin Gwamnan Hon. Faruk Jobe da Jagoran adawar, sun tattauna muhimman batutuwa da su ka shafi siyasa tare da buƙatar jagoran adawar da ya dawo cikin Jam'iyyar sa ta Apc da aka ginata dashi, domin ya k**a a ci gaba da ciyar da Jihar Katsina gaba.

Zawarcin jagoran adawar ya biyo bayan rikice, rikicen da Jam'iyyar su ta ADC take fama dasu musamman bayan zaɓukan fidda gwani, inda su ka ƙalubalanci yadda aka gudanar da zaɓen fidda gwani ba bisa ƙa'ida ta doka ba.

Yan Asalin Jihar Katsina Sun Yi Fice a Taron Matasan Najeriya Kan Sauyin Yanayi da Aka Gudanar a AbujaWasu matasa guda t...
06/06/2026

Yan Asalin Jihar Katsina Sun Yi Fice a Taron Matasan Najeriya Kan Sauyin Yanayi da Aka Gudanar a Abuja

Wasu matasa guda takwas daga Jihar Katsina sun wakilci jihar a Taron Matasan Najeriya Kan Sauyin Yanayi (National Youth Climate Summit) da aka gudanar a Abuja, wanda Sakatariyar Majalisar Kasa Kan Sauyin Yanayi (NCCC) ta shirya tare da hadin gwiwar UNICEF, ActionAid, GIZ da sauran kungiyoyi. Majalisar Sauyin Yanayi ta Jihar Katsina tare da Ma’aikatar Muhalli ta Jihar ne s**a jagoranci tawagar, wadda ta kasance mai mafi yawan matasa daga kowace jiha a taron da ya hada mahalarta sama da 200 daga sassan kasar nan domin tsara hanyoyin shigar da matasa cikin aiwatar da shirin NDC 3.0 na Najeriya.

Tawagar Katsina karkashin jagorancin Hon. Suleiman Ribadu, Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamna kan Sauyin Yanayi, da Dr. Yusha’u El-Sunais Sani na Ma’aikatar Muhalli, ta yi fice matuka ta hanyar gabatar da wani sabon tsari mai suna “Eco-Tracker”, wanda Halima Kabir Sani daga Dutsin-Ma ta kirkira. Tsarin yana taimakawa wajen bibiyar yadda makarantu da dalibai ke aiwatar da ayyukan kare muhalli da sauyin yanayi, tare da karfafa musu gwiwa ta hanyar tallafin karatu da rabon kayan koyo ga wadanda s**a yi fice. Haka kuma, tsarin na da damar samar da sahihan bayanai kan adadin iskar carbon da ake ragewa, wanda zai iya zama ginshiki ga shiga kasuwar iskar ta carbon ta Katsina da Najeriya baki daya.

Wannan nasara ta kara nuna kudurin Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, na bunkasa ayyukan kare muhalli da bai wa matasa damar taka muhimmiyar rawa wajen magance kalubalen sauyin yanayi.

Matasan da s**a halarci taron sun kuma bayyana godiyarsu ga Gwamnatin Jihar Katsina bisa goyon bayan da take bayarwa, tare da jinjinawa Dr. Mustapha Shehu wanda tallafinsa ya ba wa shida daga cikin mahalartan damar halartar taron.

MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government

June 6, 2026.

Hawan Sarki (Bariki) a Jihar KatsinaAn gudanar da bikin Hawan Sarki na babbar sallar shekarar 2026 a Jihar Katsina cikin...
28/05/2026

Hawan Sarki (Bariki) a Jihar Katsina

An gudanar da bikin Hawan Sarki na babbar sallar shekarar 2026 a Jihar Katsina cikin armashi, kima da kuma nuna ɗaukakar al’adun Hausawa da na Masarautar Katsina. Bikin, wanda aka fi sani da Hawan Bariki, ya gudana a tsohon gidan Gwamnatin Jihar Katsina tare da halartar dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma ƙasashen waje.

A yayin bikin, mahaya dawakai daga masarautar jihar Katsina sun gudanar da hawan cikin kayatattun kayan al’ada da ado na gargajiya, lamarin da ya ƙara fito da tarihi, martaba da kuma haɗin kan al’ummar Katsina. Hakimai, masu sarautun gargajiya, fadawa da sauran masu riƙe da sarautun gargajiya sun halarci bikin domin nuna biyayya da girmamawa ga masarauta da gwamnatin jihar.

Cikin masu jawabi akwai Sarkin Katsina, mai martaba Alhaji Abdulmumini Kabir Usman, wanda ya jaddada muhimmancin zaman lafiya, haɗin kai da biyayya ga doka domin tabbatar da ci gaba mai ɗorewa a jihar. Sarkin ya yaba da yadda jama’a s**a ci gaba da kare martabar al’adu da kyawawan dabi’un gargajiya, tare da kira ga al’umma su haɗa kai da gwamnati wajen tabbatar da tsaro da ci gaba.

Hakazalika, Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina ya halarci bikin a madadin naigirma gwamna tare da manyan jami’an gwamnati, ‘yan majalisar dokoki, shugabannin hukumomi da sauran masu ruwa da tsaki. Bikin ya zama wata dama ta nuna haɗin kai tsakanin gwamnati da masarautu wajen bunƙasa zaman lafiya da raya al’adu a jihar.

Bikin Hawan Sarki na bana ya samu halartar jakadun ƙasashen Turai da sauran jami’an diflomasiyya daga ƙasashe daban-daban, waɗanda s**a zo domin shaida ɗimbin al’adu, tarihi da martabar Masarautar Katsina. Jakadun sun yaba da yadda jihar ke kare al’adunta tare da ƙoƙarin inganta zaman lafiya da bunƙasa yawon buɗe ido.

Bikin ya gudana cikin lumana da tsari, inda kaɗe-kaɗe na gargajiya irin su kalangu da algaita s**a ƙara wa taron armashi, yayin da jama’a s**a cika titunan Katsina domin kallon wannan gagarumin biki na tarihi da al’adu.

MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government

May 28, 2026.

Gwamna Radda Ya Kai Ziyarar Gaisuwa Ga Mahajjatan Katsina A Mina, Alhazai Sun Nuna Farin Ciki Bisa Hadaya Da Barka Da Sa...
28/05/2026

Gwamna Radda Ya Kai Ziyarar Gaisuwa Ga Mahajjatan Katsina A Mina, Alhazai Sun Nuna Farin Ciki Bisa Hadaya Da Barka Da Sallah Da Ya Basu

Mahajjatan jihar Katsina sun tarbi Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda, cikin farin ciki da annashuwa yayin da ya kai musu ziyarar gaisuwa a masaukin su da ke Mina, gabanin kammala aikin Hajjin shekarar 2026.

Alhazan sun bayyana jin daɗin su da godiyar su bisa kuɗin Hadaya da Gwamnan ya biya musu tare da kyautar Barka da Sallah ta Riyal 300 da ya rabawa kowane mahajjaci.

A yayin ziyarar, tawagar malaman lafiya da gwamnatin jihar Katsina ta tura domin kula da lafiyar mahajjata sun kuma gudanar da duba lafiyar Gwamnan a ɗakin kula da lafiyar alhazai da ke Mina.

Shugaban Alhazan jihar Katsina (Amirul Hajji), Barista Ahmed Usman El-Marzuq, ne ya tarbi Gwamnan tare da jagorantar zagayawarsa tanti zuwa tanti domin gaishe da mahajjatan da kuma taya su murnar samun damar gudanar da aikin Hajji bana.

Gwamna Radda ya bukaci alhazan da su ci gaba da sanya jihar Katsina cikin addu’o’insu domin samun zaman lafiya, ci gaba da ɗorewar haɗin kai a jihar.

Mahajjatan sun yi addu’o’i na musamman ga Gwamnan bisa kulawar da yake bai wa alhazan jihar Katsina, musamman wajen biya musu Hadaya da kuma tallafin Barka da Sallah da ya ba su yayin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026.

MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government

May 28, 2026.

HOTUNAYadda aka gudanar da bikin hawan idin babbar sallah a jihar Katsina. Mataimakin gwamnan jihar Katsina, Malam Farou...
27/05/2026

HOTUNA

Yadda aka gudanar da bikin hawan idin babbar sallah a jihar Katsina.

Mataimakin gwamnan jihar Katsina, Malam Farouk Lawal Jobe shi ya jagoranci bikin taro da halartar manyan baki ciki hadda turawa daga kasashen daban-daban na fadin duniya.

An bayyana kawa da kasaita cikin ado da kuma burgewa inda hakimai da sauran mahaya s**a kayatar da yan kallo.

Address

Katsina

Telephone

+2349039416720

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when APC Social Media Organisation Katsina State posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to APC Social Media Organisation Katsina State:

Share