Engr. Sagir Ibrahim Koki

Engr. Sagir Ibrahim Koki Member, Kano Municipal Federal Constituency, Deputy Chairman, House Committee on Petroleum Midstream.

Muna farin cikin sanar da al’umma cewa mun samu nasarar rabawa ɗaliban Dan Agundi Special Primary School littattafai sam...
21/09/2025

Muna farin cikin sanar da al’umma cewa mun samu nasarar rabawa ɗaliban Dan Agundi Special Primary School littattafai sama da 2000 ta hannun Comr. Abdulhakim Kumbotso, karkashin jagorancin Kungiyar Daliban Dan Agundi. Wannan wani ƙoƙari ne na kawo ci gaba ga al’umma, musamman ma a bangaren ilimi, wanda ke daga cikin abubuwan da muke baiwa muhimmanci a cikin yankinmu.

Malamai da ɗalibai na makarantar sun nuna matuƙar farin ciki da godiya ga wannan tallafi. A matsayina na ɗaya daga cikin wakilan al’umma, wannan na daga cikin ƙoƙarinmu na kawo wa al'ummar yankinmu ci gaba mai dorewa.-SIK

A ƙoƙarin mu na ganin an samu ci gaba a fannin lafiya da ilimi musamman ga mata 'yan asalin Kano Municipal, mun dauki na...
11/09/2025

A ƙoƙarin mu na ganin an samu ci gaba a fannin lafiya da ilimi musamman ga mata 'yan asalin Kano Municipal, mun dauki nauyin wasu dalibai daga Adamu Adamu College of Nursing and Science domin su samu damar karatu.

Wannan mataki yana daga cikin himmarmu na tallafawa matasa wajen cika burinsu na zama kwararru a fannin lafiya. Yanzu haka, daliban na shirin fara karatunsu cikin kwanciyar hankali da fatana su zama ginshikan ci gaban al'umma.

Muna rokon Allah ya sa wannan aiki ya zamo alheri a gare su da al’umma baki ɗaya. Za mu ci gaba da ƙoƙarin ganin matasanmu sun samu mafita mai dorewa Insha Allah.-SIK

Alhamdulilah Mun samu damar gudanar da ibadah a Madina cikin sauki da rahamar Ubangiji. Yanzu muna kan hanyarmu zuwa Mak...
10/09/2025

Alhamdulilah Mun samu damar gudanar da ibadah a Madina cikin sauki da rahamar Ubangiji. Yanzu muna kan hanyarmu zuwa Makkah domin Umrah. Allah ya karɓa, ya sa hakan ya zama hujja a garemu, ba hujja a kanmu ba.

Allah ya amsa, ya karɓa, ya maimaita mana cikin alheri.-SIK

Alhamdulillah! A ci gaba da kokarin tallafa wa matasa 'yan asalin Karamar Hukumar Birnin Kano, musamman 'yan mata masu s...
09/09/2025

Alhamdulillah! A ci gaba da kokarin tallafa wa matasa 'yan asalin Karamar Hukumar Birnin Kano, musamman 'yan mata masu sha'awar ilimin kiwon lafiya, mun dauki nauyin wasu dalibai mata 10 zuwa Adamu Adamu College of Nursing Sciences, Azare – Bauchi, inda za su fara karatun kiwon lafiya.

Inda cikin yardar Allah muka dauki nauyin dukkanin bukatunsu: kudin makaranta, litattafai, kayan karatu, kudin kashewa da kuma na’ura mai kwakwalwa domin tallafa musu wajen karatunsu.

Wannan tafiya ta samu cikakken rakiya karkashin jagorancin wasu daga cikin wakilanmu, waɗanda s**a tabbatar da tsaron da jagorantar ɗaliban.

Wakilanmu ne s**a raka su har zuwa makarantar, kuma muna roƙon Allah Ya ba su nasara, Ya kuma saka musu da alheri bisa wannan hidima da s**a ɗauka domin ci gaban al’umma.-SIK

Alhamdulillah! A ci gaba da ƙoƙarin tallafa wa matasa, musamman 'yan mata masu sha'awar ilimin jinya, a jiya Asabar 06/0...
07/09/2025

Alhamdulillah! A ci gaba da ƙoƙarin tallafa wa matasa, musamman 'yan mata masu sha'awar ilimin jinya, a jiya Asabar 06/09/2025, mun sake ɗaukar nauyin wasu dalibai mata 12 zuwa Adamu Adamu College of Nursing Science, Azare, inda s**a karɓi takardun shaidar amincewa da su (admission) domin fara karatu.

Daga farkon wannan shiri zuwa yanzu, adadin daliban da muka dauki nauyin karatunsu ya kai 42:

- 24 na karatu a Nafisatu College of Nursing and Midwifery, Madobi
- 18 a Adamu Adamu College of Nursing Science, Azare

Wannan wani bangare ne na ƙudurorinmu na ganin matasanmu – musamman 'yan mata – sun samu damar ci gaba da karatu domin gina makoma mai kyau.-SIK

Alhamdulilah Jiya, mun kaddamar da sabon Bohole a mazabar Yakasai, dake karamar hukumar Birni,domin samar da ruwan sha m...
06/09/2025

Alhamdulilah Jiya, mun kaddamar da sabon Bohole a mazabar Yakasai, dake karamar hukumar Birni,
domin samar da ruwan sha mai tsafta ga jama’a da rage musu wahala.

Wannan wani muhimmin mataki ne a tafarkin da muka sa gaba na ci gaba mai ɗorewa.

Allah ya bamu ikon Sauke Nauyin Al’ummar dake kan mu.-SIK

Alhamdulillah, an kammala aikin bude sabon rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana (solar) a unguwar Zage, cikin maz...
03/09/2025

Alhamdulillah, an kammala aikin bude sabon rijiyar burtsatse mai amfani da hasken rana (solar) a unguwar Zage, cikin mazabar Zango, karamar hukumar Birni — wanda muka samar domin rage wa al’umma wahalar samun ruwa, musamman mata da yara.

Wannan muhimmin aiki an kaddamar da shi ne a hukumance ta hannun Hon Saifullahi Hassan, dan unguwar da kuma jigo a cikin al’umma, wanda ya jagoranci bikin kaddamarwar.

Muna mika godiya ga daukacin jama’ar da s**a halarta domin shaida wannan aiki. Wannan na daga cikin ayyukan ci gaba da nake kokarin kawowa ga al’umma, domin tabbatar da saukin rayuwa da ingancin ababen more rayuwa.

Allah ya saka da alheri, ya kuma bamu ikon ci gaba da yi wa jama’a hidima da gaskiya da amana.-SIK

Alhamdulillah Ina mika godiya ta musamman ga dukkan ’yan uwa, abokai da baki na musamman da s**a halarta bikin auren ’ya...
31/08/2025

Alhamdulillah Ina mika godiya ta musamman ga dukkan ’yan uwa, abokai da baki na musamman da s**a halarta bikin auren ’yata, Fatima Abdullahi Garba Koki.

Allah Ya saka wa kowa da alheri , musamman Mai girma Mataimakin Gwamnan Kano, HE Comr. Aminu Abdulsalam, Sanata Rufai Sani Hanga, da abokaina na Majalisar Wakilai.

Allah Ya kara ɗaukaka da albarka a rayuwarku.-SIK

Alhamdulillah, a jiya kenan muka kai ziyarar ban girma a ofishin Kwamishinan Harkokin Kasuwanci da Sana’o’i, na Jihar Ka...
29/08/2025

Alhamdulillah, a jiya kenan muka kai ziyarar ban girma a ofishin Kwamishinan Harkokin Kasuwanci da Sana’o’i, na Jihar Kano. Alhaji Shehu Wada Sagagi. Allah Ya kara dafa mana Ameen.-SIK

Cikin ikon Allah mun kai ziyarar ta’aziyyar rasuwa a gidan Marigayi Alhaji Dan Dawaki dake mazabar Shahuci. Allah Ya jik...
29/08/2025

Cikin ikon Allah mun kai ziyarar ta’aziyyar rasuwa a gidan Marigayi Alhaji Dan Dawaki dake mazabar Shahuci. Allah Ya jikan musulmi gaba ɗaya, Allah Ya haskaka makwancinsa, Ya kuma ba ‘yan uwa da iyalai juriyar rashin.-SIK

Cikin ikon Allah mun kai ziyarar ta’aziyya ga dangin marigayiya, mahaifiyar Alhaji Aminu Joker, wace Allah Ya yi wa rasu...
28/08/2025

Cikin ikon Allah mun kai ziyarar ta’aziyya ga dangin marigayiya, mahaifiyar Alhaji Aminu Joker, wace Allah Ya yi wa rasuwa a Mazabar Tudun Wuzirchi. Allah Ya jikanta da rahama da gafara, Ya sanya ta huta cikin rahamarsa.

Muna roƙon Allah Ya ba iyalanta haƙuri da juriya a kan wannan rashi, Ya tsare su da zaman lafiya da ɗaukaka.-SIK

Cikin ikon Allah na samu damar halartar bikin yaye ɗalibai da cikar shekaru 10 ta makarantar Maryam Aloma Girls Secondar...
25/08/2025

Cikin ikon Allah na samu damar halartar bikin yaye ɗalibai da cikar shekaru 10 ta makarantar Maryam Aloma Girls Secondary School. A yayin taron, aka karramani da lambar yabo a matsayin girmamawa bisa gudummawata ga makarantar.

Ina roƙon Allah Ya cigaba da albarkaci wannan makaranta tare da ɗaliban da take yaye wa.-SIK

Address

Abuja
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Engr. Sagir Ibrahim Koki posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share