National Youth Council of Nigeria Kumbotso Local Government Chapter

  • Home
  • Nigeria
  • Kano
  • National Youth Council of Nigeria Kumbotso Local Government Chapter

National Youth Council of Nigeria Kumbotso Local Government Chapter Build the youth, build the Nation

23/04/2026

Shugaban Majalisar Matasan Ƙaramar Hukuma ya buƙaci matasa su fito su yi katin zaɓe.

Alhmdllh..Yau Litinin, 6 ga watan Afrilu (April), 2026, Majalisar Matasan Karamar Hukumar Kumbotso (NYCN) ta zauna zaman...
06/04/2026

Alhmdllh..

Yau Litinin, 6 ga watan Afrilu (April), 2026, Majalisar Matasan Karamar Hukumar Kumbotso (NYCN) ta zauna zaman Council Meeting kamar yadda aka saba.

Zaman ya gudana cikin nasara da lumana, inda aka tattauna muhimman batutuwa da s**a shafi cigaban matasa da al’umma baki ɗaya.

An jaddada muhimmancin haɗin kai da zaman lafiya, tare da ƙudurin ci gaba da aiki tuƙuru domin inganta rayuwar matasa.

AlhamdulillahToday marks one full year since we were inaugurated as leaders of the National Youth Council of Nigeria (NY...
26/03/2026

Alhamdulillah

Today marks one full year since we were inaugurated as leaders of the National Youth Council of Nigeria (NYCN), Kumbotso Chapter. This year has been full of challenges and achievements, all under the guidance of Allah (SWT).

We are grateful for life, health, and the ability to serve the youth and our community.

May Allah grant us the grace to complete the rest of our years in good health, peace, and success.

Bashir Sanata Zwk
Public Relations Officer,
NYCN Kumbotso Chapter

SAKON GODIYAMajalisar Matasan Karamar Hukumar Kumbotso tana mika sakon godiya na musamman ga mai girma Shugaban Karamar ...
18/03/2026

SAKON GODIYA

Majalisar Matasan Karamar Hukumar Kumbotso tana mika sakon godiya na musamman ga mai girma Shugaban Karamar Hukumar Kumbotso, Comrd. Abdullahi Ghali Basaf , bisa irin tallafin Azumi da ya bai wa majalisar, wanda ya hada da buhunan shinkafa da taliya domin tallafawa matasa a wannan wata mai alfarma na Ramadan.

Wannan karamci da kulawa da yake nunawa matasa na kara tabbatar da irin jajircewarsa wajen inganta rayuwar al’umma, musamman matasa a fadin karamar hukumar Kumbotso.

Muna addu’ar Allah ya saka masa da alheri, ya kara masa lafiya da karfin guiwa domin ci gaba da yi wa al’ummar Kumbotso hidima. Allah ya sanya wannan tallafi ya zama alheri a gare shi.

‎National Youth council of Nigeria kumbotso local government Chapter under the leadership of its Chairman, Comr. Ahmad T...
17/02/2026

‎National Youth council of Nigeria kumbotso local government Chapter under the leadership of its Chairman, Comr. Ahmad Tijjani Muhd, congratulates the newly elected executives of the Kumbotso Local Government Students Association (KUMBOSA) on their victory in the recently conducted election.

‎This achievement is not a small responsibility, as you have been entrusted with the duty of leading the students of Kumbotso with honesty, integrity, and a strong commitment to educational development. We are confident that you will work diligently to protect the interests of the students while promoting unity and progress among them.

‎The NYCN kumbotso assures you of its full support and cooperation in any initiative that will bring development to students and the entire people of Kumbotso.

‎We pray that Almighty God grants you the ability to carry out this responsibility effectively, and blesses you with wisdom and perseverance in the successful discharge of your duties.

‎Signed:
‎Comr. Ahmad Tijjani Muhd
‎Chairman, NYCN Kumbotso
‎Local Government

Majalisar Matasan Karamar Hukumar Kumbotso ta gudanar da zaman Council Meeting a yau, inda aka tattauna batutuwa masu mu...
29/01/2026

Majalisar Matasan Karamar Hukumar Kumbotso ta gudanar da zaman Council Meeting a yau, inda aka tattauna batutuwa masu muhimmanci kan ci gaban matasa da ƙarfafa haɗin kai a cikin ƙaramar hukumar. Zaman ya gudana lafiya tare da cimma matsaya mai amfani. 📌💪





‎KUMBOTSO TA KAMMALA RAJISTAR SHIRIN RENEWED HOPE WARD DEVELOPMENT PROJECT‎‎Ƙaramar Hukumar Kumbotso ta kammala aikin ra...
22/01/2026

‎KUMBOTSO TA KAMMALA RAJISTAR SHIRIN RENEWED HOPE WARD DEVELOPMENT PROJECT

‎Ƙaramar Hukumar Kumbotso ta kammala aikin rajistar Shirin Renewed Hope Ward Development Project, shiri ne na tallafi da aka tsara domin amfanar dubunnan al’umma daga kowace mazaɓa, ta hanyar bunƙasa tattalin arziki da rayuwar jama’a a matakin ƙasa.

‎Muna sanar da al’umma cewa wannan shiri ba ya amfani da kowanne link. Jami’an da aka amince da su (Enumerators) su ne kaɗai ke da damar ɗaukar bayanan masu rajista.

‎Don haka, kada ku yarda da duk wani link da za a turo muku da sunan cika wannan shiri, domin hakan zamba ne (scam). Sau da yawa, idan aka fitar da irin waɗannan shirye-shirye, masu damfara kan ƙirƙiri hanyoyi domin yaudarar jama’a.

‎Muna jan hankalin al’umma da su yi hattara, ko a cikin group ko a wani wuri, duk wanda kuka ga yana yaɗa link da sunan wannan shiri, ku sani ba sahihi ba ne.

‎Za a sanar da jama’a a hukumance idan aka sake buɗe ɗaukar bayanai karo na gaba domin amfana da wannan tallafi.

‎✍🏻
Comr. Ahmad Tijjani Muhammad
‎Coordinator
‎Renewed Hope Ward Development Project
‎Kumbotso Local Government

‎SANARWA GA AL’UMMAR KUMBOTSO ‎‎Ana sanar da al’ummar Karamar Hukumar Kumbotso cewa a halin yanzu ana ci gaba da rajista...
16/01/2026

‎SANARWA GA AL’UMMAR KUMBOTSO

‎Ana sanar da al’ummar Karamar Hukumar Kumbotso cewa a halin yanzu ana ci gaba da rajistar Shirin Renewed Hope, wani shiri na musamman da aka kawo domin tallafa wa ‘yan ƙasa da inganta rayuwar jama’a.

‎Dukkan mazauna mazabun Kumbotso guda 11 da ke sha’awar cin gajiyar wannan shiri, ana kira gare su da su tuntuɓi Coordinator na mazabarsu domin yin rajista.

‎👉 Abubuwan da ake buƙata:

‎Cikakken Suna : Full Name

‎National Identification Card (NIN)

‎Lambar Wayar Hannu (Phone Number)

‎Shekarun Haihuwa ( Date of birth )

‎💡 Kada a bari wannan dama ta wuce ka! A sanar da dangi, abokai da makwabta domin kowa ya amfana.

‎NB : kyauta ne kar wani yace ka bada kudi ya cike maka a tunutubi coordinator mazabu

‎COORDINATOR KUMBOTSO LOCAL GOVERNMENT
‎📞 09036178098

‎ 📍 Mazabu da Lambobin Tuntuɓa

‎FANSHEKARA
‎📞 09122946835
‎📞 07049843414

‎NAIBAWA
‎📞 08064709112
‎📞 08165410512

‎DAN MALIKI
‎📞 09036178098
‎📞 0912 691 9108

‎KUREKENSANI
‎📞 08142744799

‎MARIRI
‎📞 07042391005
‎📞 0706 898 5984

‎GURIN GAWA
‎📞 08050504140
‎📞 0703 574 5331

‎CHIRANCHI
‎📞 08034856681

‎DAN BARE
‎📞 07049570153
‎📞 0803 421 3848

‎UNGUWAR RIMI
‎📞 07026113521

‎KUMBOTSO
‎📞 08146050788

‎CHALLAWA
‎📞 0906 762 3068

‎Wannan aikin yana karkashin kulawar:
‎Majalisar Matasa ta Kasa (NYCN), Reshen Karamar Hukumar Kumbotso.

‎Bashir Sanata Zawachiki
‎Public Relations Officer NYCN.✍️

‎Na samu damar halartar bikin yaye daliban shirin horaswa da koyon sana’o’i ga matasa, wanda ƙungiyar matasan Danladi Na...
05/01/2026

‎Na samu damar halartar bikin yaye daliban shirin horaswa da koyon sana’o’i ga matasa, wanda ƙungiyar matasan Danladi Nasidi multi link da ke Mazabar Mariri, Ƙaramar Hukumar Kumbotso, s**a shirya. Wannan biki ya kasance abin alfahari da farin ciki, domin ya nuna yadda al’umma ke ba da muhimmanci ga cigaban matasa ta hanyar koya musu sana’o’in dogaro da kai.

‎A yayin jawabi na, na miƙa godiya ta musamman ga dattijan wannan unguwa bisa irin cikakken goyon baya da kulawa da s**a bai wa wadannan matasa. Hakika rawar da dattijai s**a taka wajen ƙarfafa gwiwar matasa su rungumi sana’o’i abin a yaba ne, domin hakan zai taimaka matuƙa wajen rage zaman banza da dogaro da wasu, tare da gina matasa masu anfani ga kansu da al’umma baki ɗaya.

‎Haka kuma, na yaba ƙwarai da gaske ga malamai da masu koyar da wadannan sana’o’i bisa jajircewarsu, haƙuri da kishin da suke nuna wa matasa. Irin wannan sadaukarwa daga gare su shaida ce cewa har yanzu akwai mutanen da ke ɗaukar ilimi da koyar da sana’a a matsayin hidima ga al’umma. Gudummawar su ba kawai ilimi ba ce, har ma gina makomar matasa mai inganci domin su dogara da kansu

‎Bugu da ƙari, na yi kira ga sauran mazabu da ƙungiyoyin matasa a faɗin Ƙaramar Hukumar Kumbotso da su yi koyi da wannan kyakkyawan tsari. Samar wa matasa hanyoyin koyon sana’o’i da dogaro da kai shi ne ginshiƙin cigaban al’umma, domin matashin da ya samu sana’a ya samu makoma, ya samu mutunci, kuma ya zama ginshikin zaman lafiya da ci gaba.

‎Na kuma taya Hon Kamaludden Abubakar Baba wakilin shugaban karamar hukumar kumbotso comrd Abdullahi ghali basaf karbar lambar girmamawa ( graphic award) da daliban wannan makaranta wanda s**a koyi graphic s**a yiwa shugaban bisa irin gudummawar da yake bawa matasan karamar hukumar kumbotso

‎A ƙarshe, ina tabbatar wa wannan ƙungiya da dukkan mahalarta cewa a ƙarƙashin Majalisar Matasan Ƙaramar Hukumar Kumbotso, za mu ba da duk wata gudummawa da goyon baya gwargwadon iko domin ƙarfafa wannan gagarumin ƙoƙari da suke yi na tallafa wa matasa. Domin kuwa wannan shi ne burinmu tun farko na ganin matasanmu sun samu ilimi, sana’a, da kyakkyawar rayuwa mai ɗorewa.

‎Allah Ya saka wa kowa da alheri, Ya kuma albarkaci wannan shiri na tallafawa matasa

‎~ Comr. Ahmad Tijjani Muhd
‎Shugaban Majalisar Matasan
‎Ƙaramar Hukumar Kumbotso

Condolence Message from the Kumbotso Youth CouncilThe Kumbotso Local Government Youth Council extends its heartfelt cond...
26/12/2025

Condolence Message from the Kumbotso Youth Council

The Kumbotso Local Government Youth Council extends its heartfelt condolences and sympathy over the passing of two members of the Kano State House of Assembly, the late Hon. Aminu Sa’idu, Member representing Ungoggo, and the late Hon. Sarki Aliyu Daneji, Member representing Kano Municipal.

This is a great loss to Kano State as a whole, as they were leaders known for their commitment, dedication, and selfless service to the people. We convey our deepest sympathies to the Kano State Government, the Kano Emirate, the families of the deceased, and the people of Ungoggo Local Government Area and Kano Municipal.

We pray that Almighty Allah forgives their shortcomings, grants them Aljannatul Firdaus, and gives their families and the people of Kano the strength and patience to bear this irreparable loss.

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakatuh,Ina mika gaisuwar Juma’a ga al’ummar Kumbotso baki ɗaya, musamman matasa maz...
26/12/2025

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wabarakatuh,

Ina mika gaisuwar Juma’a ga al’ummar Kumbotso baki ɗaya, musamman matasa maza da mata. Ina roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya karɓi ibadunmu, Ya gafarta mana kura-kuranmu, Ya sa mu dace a maganganunmu da ayyukanmu.

Juma’a rana ce mai albarka da ke tunatar da mu muhimmancin gaskiya, hakuri, zaman lafiya da haɗin kai. Ina kira ga matasan Kumbotso da su ci gaba da zama masu bin doka da oda, su guji duk wani abu da zai kawo cikas ga zaman lafiya da ci gaban al’umma. Mu kasance jakadun kirki, mu taimaki juna, mu girmama manya, mu tausaya wa ƙanana.

Ina kuma ƙarfafa matasa da su rungumi ilimi, sana’o’i da ƙwarewa, domin su dogara da kansu, su zama masu amfani ga kansu da al’ummarsu. Mu yi aiki tare da shugabanni domin gina Kumbotso mai albarka, tsaro da cigaba.

Allah Ya sa wannan Juma’a ta zamo sanadiyyar alheri, zaman lafiya da nasara a gare mu baki ɗaya.

Juma’a Mubarak!

Comrd. Ahmad Tijjani Muhammad
Shugaban Majalisar Matasan Kumbotso

Address

Sheka
Kano
700101

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when National Youth Council of Nigeria Kumbotso Local Government Chapter posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share