Amanar Talaka TV

Amanar Talaka TV We are here to mobilize, to deliver for you, all about Kano, Nigeria's Politics and more 💯🇳🇬

Contact: 07055024493/07066857138

REMASAB ta karyata zargin rashin biyan Æ´an shara albashin su Hukumar Kula da tsaftar muhalli da kwashe shara ta Jihar Ka...
02/06/2026

REMASAB ta karyata zargin rashin biyan Æ´an shara albashin su

Hukumar Kula da tsaftar muhalli da kwashe shara ta Jihar Kano (REMASAB) ta karyata rahotannin da ke ikirarin cewa ba ta biyan ma’aikatanta albashi, tare da zargin cewa wasu ma’aikatan na karɓar Naira 10,000 kacal a kowane wata.

A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Abubakar Ahmad, ya fitar ranar 2 ga Yuni, 2026, REMASAB ta ce zarge-zargen da aka wallafa a wani flyer na shafin Facebook na gidan rediyon Dala FM ƙarya ne kuma ba su da alaƙa da ainihin halin da ake ciki a hukumar.

Hukumar ta bayyana cewa babu wani ma’aikacinta da ke karɓar albashin Naira 10,000, tare da ƙalubalantar duk wanda ke da irin wannan da’awa da ya gabatar da shaidar biyan albashinsa ga hukumar ko ga kafar yaɗa labaran da ta wallafa zargin.

REMASAB ta nuna damuwa kan yadda aka yaɗa rahoton ba tare da neman ƙarin bayani ko tabbatar da gaskiyar lamarin daga hukumarta ba, tana mai cewa hakan ya saɓa wa ƙa’idojin aikin jarida na gaskiya, adalci da ƙwarewa.

Hukumar ta kuma bukaci Dala FM da sauran masu yaÉ—a rahoton su gabatar da hujjojin da s**a dogara da su wajen wallafa zarge-zargen, tare da neman a janye rahoton da kuma gyara bayanan da aka wallafa.

A cewar sanarwar, REMASAB na ci gaba da biyan albashin ma’aikatanta a kai a kai ba tare da jinkiri ba, sannan ta ce ta biya duk wasu basuss**an albashi da ta gada, inda ta jaddada cewa a halin yanzu babu wani ma’aikacin hukumar da ake bin sa albashi.

Hukumar ta yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su riƙa tabbatar da sahihancin bayanai kafin wallafawa domin kauce wa yaɗa labaran da ba su da tushe.

Daily Nigerian Hausa

Hukumar civil defense ta kori ma’aikatan ta na sa-kai su biyar a KanoHukumar Tsaron ta Farar Hula ta Kasa (NSCDC) reshen...
02/06/2026

Hukumar civil defense ta kori ma’aikatan ta na sa-kai su biyar a Kano

Hukumar Tsaron ta Farar Hula ta Kasa (NSCDC) reshen jihar Kano ta sallami ma’aikatan sa-kai biyar daga aiki bisa zargin rashin da’a da rashin ƙwarewar aiki da kuma rashin ladabi.

Waɗanda abin ya shafa sun haɗa da Yakubu Mubarak Yusuf, Isma’il Muhammad, Adamu Auwalu, Abdulrazaq Suleiman da Ahmad Sarki.

Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar NSCDC a Kano, Ibrahim Abdullahi, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata.

Sanarwar ta ce Kwamandan NSCDC na jihar Kano, Mohammed Agalama, ya amince da sallamar ma’aikatan bayan nazarin laifukan da ake zarginsu da aikatawa, waɗanda aka gano sun saɓa wa ƙa’idoji, ɗabi’u da kuma matakan gudanar da ayyukan hukumar.

Hukumar ta kuma bayyana cewa an ƙwace dukkan kayan aiki, kayan sawa na aiki, katunan shaida da sauran kayayyakin da ma’aikatan ke amfani da su.

Kwamandan ya umarci kwamandojin yankuna, shugabannin ofisoshin ƙananan hukumomi da sauran jami’ai masu ruwa da tsaki a faɗin jihar da su tabbatar ba a sake amincewa ko ɗaukar waɗannan mutane a matsayin wakilan NSCDC ba.

GWAMNAN JIHAR KANO YA AMINCE DA HAÆŠE MA'AIKATAR MUHALLI DATA RUWA.Kwamishinan da ke rikon ma'aikatar ruwan na Kano kuma ...
01/06/2026

GWAMNAN JIHAR KANO YA AMINCE DA HAÆŠE MA'AIKATAR MUHALLI DATA RUWA.

Kwamishinan da ke rikon ma'aikatar ruwan na Kano kuma kwamishinan ma'aikatar muhalli Dakta Dahir Muhammad Hashim ne ya bayyana hakan, yayin wata ziyarar duba aiki da ya kai, a matattarar ruwa da le Goron dutse.

Ya ce sakamakon korafe-korafen da al'ummar Kano ke Yi na rashin ruea ya sa gwamnan Kanon injiniya Abba Kabir Yusuf ya Tashi tsaye wajan ganin an magance matsalar.

Dr Dahir ya Kuma ce akwai matattarar ruwan da an kai shekara talatin ba a zuba mata ruwa ko Lita daya ba a Goron Dutsen. A don haka ya ce za su yi duk mai yiwuwa wajan ganin an magance matsalar ruwan a Yan watannin nan.

Idan ba za a manta ba dai tun a kwanakin baya ne gwamnatin Kano ta kaddamar da shirin ta na gyare-gyare a bangaren ruwan wanda zai ci Sama da biliyan sha daya.

Ƙungiyar ta ce idan aka yi duba da halin da ake ciki na tsadar rayuwa a ƙasar ya kamata a ƙalla a riƙa biyan ma'aikata m...
01/06/2026

Ƙungiyar ta ce idan aka yi duba da halin da ake ciki na tsadar rayuwa a ƙasar ya kamata a ƙalla a riƙa biyan ma'aikata mafi ƙarancin albashi na naira miliyan daya.

Ƙarin bayani - BBC Hausa

Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar, ya yi watsi da zargin da tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babach...
01/06/2026

Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya, Atiku Abubakar, ya yi watsi da zargin da tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ya yi cewa an tafka magudi a zaben fidda gwani na jam'iyyar ADC

Jaridar Punch ta ruwaito ofishin yada labaran Atiku, ya ce babu wata hujja da ke tabbatar da zargin, kuma sun bayyana kalaman Babachir a matsayin zarge-zarge marasa tushe da kuma rashin adalci a siyasa.

Garkuwa da Mutane: Tinubu Ya Amince da Daukar Masu Tsaron Daji 1,000 a Jihar Oyo, Ya Tura Tawagar CetoShugaba Bola Tinub...
31/05/2026

Garkuwa da Mutane: Tinubu Ya Amince da Daukar Masu Tsaron Daji 1,000 a Jihar Oyo, Ya Tura Tawagar Ceto

Shugaba Bola Tinubu ya amince da ɗaukar masu tsaron daji 1,000 a Jihar Oyo a matsayin wani ɓangare na matakan ƙarfafa tsaro bayan sace ɗalibai da malamai da aka yi a jihar.

An sanar da amincewar ne a lokacin wata ziyara da wata babbar tawagar Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Mista Femi Gbajabiamila, Babban Ma’aikacin Fadar Shugaban Ƙasa, ta kai garuruwan Ahoro-Esinele da Yawota da ke kusa da Ogbomoso a Ƙaramar Hukumar Oriire ranar Lahadi.

Tawagar ta kuma kai ziyarar ne domin duba halin da ake ciki tare da isar da saƙon ta’aziyya da goyon bayan Gwamnatin Tarayya kan lamarin garkuwa da mutanen.

Shin an taɓa ɗaukar irin wannan mataki kuwa a Arewa?

Nafiu Bala ya jaddada cewa har yanzu Atiku Abubakar ba dan jam’iyyar ADC bane, don haka tsayar da shi takarar shugaban k...
31/05/2026

Nafiu Bala ya jaddada cewa har yanzu Atiku Abubakar ba dan jam’iyyar ADC bane, don haka tsayar da shi takarar shugaban kasa kamar wasan kwaikwayo ne.

A cewarsa tsagin David Mark basu da hurumin tsayar da dan takara, domin ba sune halastattun shugabannin jam’iyyar ba.

Nafiu Bala ya kara da cewa nan gaba kadan kotu za ta yanke hukuncin karshe, tare da ayyana shi a matsayin halastaccen shugaban jam’iyyar ADC na kasa.

31/05/2026

Allah ya bamu lafiya da zama lafiya a wannan ƙasa tamu baki ɗaya ta Nigeria.

Obi ya ce idan ya ci zaɓen shekarar 2027, zai yi aiki kafada-kafada da mataimakin sa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso
31/05/2026

Obi ya ce idan ya ci zaɓen shekarar 2027, zai yi aiki kafada-kafada da mataimakin sa, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso

Na yi nasarar sauke kaso 90 cikin 100 na alkawuran da na yi wa mutanen jihar Kano - Gwamna Abba Kabir YusufKun amince ko...
30/05/2026

Na yi nasarar sauke kaso 90 cikin 100 na alkawuran da na yi wa mutanen jihar Kano - Gwamna Abba Kabir Yusuf

Kun amince ko kuna da shakku?

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Amanar Talaka TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share