25/05/2026
Tofa kajiwa magana awajan...........?
Uwar Gidan Shugaban Ƙasa Tinubu Ta Yi Kira Da A Gaggauta Kawo Ƙarshen Auren Wuri A Najeriya
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Oluremi Tinubu, ta yi kira da a kawo ƙarshen auren yara ƙanana tare da inganta kula da lafiyar mata masu juna biyu domin rage yawaitar cutar fistula a Najeriya.
Ta bayyana hakan ne yayin tunawa da Ranar Yaƙi da Cutar Fistula ta Duniya, inda ta ce auren yara da ɗaukar ciki tun suna ƙanana na daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa cutar, kamar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito.
Oluremi Tinubu ta kuma buƙaci a ƙarfafa ilimin mata da tabbatar da cewa kowace mace ta samu ingantacciyar kulawar lafiya yayin haihuwa.
Rahotanni sun nuna cewa dubban mata ne ke fama da cutar fistula a Najeriya, musamman a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas.