20/07/2026
SAƘO ZUWA GA DUKKAN SHUGABANNIN ƘARAMAR HUKUMAR UNGOGO
Wannan saƙo ne zuwa ga Shugaban Ƙaramar Hukuma, Ɗan Majalisar Tarayya, Ɗan Majalisar Jiha, da duk wani shugaba da aka zaɓa domin wakiltar al'ummar Ƙaramar Hukumar Ungogo.
A gaskiya, al'ummar Ungogo sun gaji da alƙawura ba tare da ganin ayyukan ci gaba ba. Tun daga shekarar 1999 zuwa yau, mutane da dama na ganin ƙaramar hukumar mu ta yi baya idan aka kwatanta da wasu ƙananan hukumomi. Hanyoyi, kiwon lafiya, ilimi, ruwa, hasken t**i da sauran muhimman abubuwan more rayuwa har yanzu suna buƙatar kulawa sosai.
Lokaci ya yi da shugabanni za su saurari kukan al'umma, su mayar da hankali kan ayyuka masu amfani maimakon alƙawuran da ba su cika ba.
Muna sanar da ku cewa idan ba a ga ingantaccen sauyi da ayyukan ci gaba ba kafin zaɓen 2027, al'ummar Ungogo za su yi amfani da haƙƙinsu na dimokuraɗiyya wajen zaɓar waɗanda suke ganin za su fi yi musu aiki.
Kuri'ar al'umma amana ce, kuma za a ba ta ne ga wanda ya nuna aiki, gaskiya, da kishin cigaban Ungogo.
Allah Ya ba mu shugabanni nagari, Ya kuma sa Ungogo ta samu ci gaban da ya dace.