A M T Hausa

A M T Hausa Journalists by profession accurate information 24/7

Fadi muji : Gwamnatina ta cika kashi 90 cikin 100 na alkawuran da ta yi wa al'ummar Jihar Kano cikin shekaru uku da ta s...
31/05/2026

Fadi muji : Gwamnatina ta cika kashi 90 cikin 100 na alkawuran da ta yi wa al'ummar Jihar Kano cikin shekaru uku da ta shafe tana mulki -

Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka ne a ranar Asabar yayin da yake karɓar bakuncin Sarkin Rano, Ambasada Muhammad Isa Umaru, wanda ya kai masa gaisuwar Sallah a Fadar Gwamnatin Kano.

Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnatin sa ta samu manyan nasarori a fannoni daban-daban, tare da jaddada aniyarta na ci gaba da aiwatar da sauran alkawuran da s**a rage domin inganta rayuwar al'ummar jihar.

Shin wannan batu nashi haka yake?

Bayan zaben fidda Gwani na Jam'iyar APC A jihar kaduna An sami Rabuwar kai tsa kanin wasu daga cikin jagorin martanin sh...
30/05/2026

Bayan zaben fidda Gwani na Jam'iyar APC A jihar kaduna An sami Rabuwar kai tsa kanin wasu daga cikin jagorin martanin shehu sani ga Abokin ta karrar sa yusuf zailani

Sanata Rufa’i Hanga,  ya bayyana cewa babu abin da zai raba shi da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso.A wata hira da yayi da w...
30/05/2026

Sanata Rufa’i Hanga, ya bayyana cewa babu abin da zai raba shi da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso.

A wata hira da yayi da wani gidan jarida ta wayar tashi, Hanga ya ce da amincewar sa aka baiwa Dr Nasiru Yusuf Gawuna takarar kujerar Sanatan Kano ta tsakiya.

Hanga ya ƙara da cewa, babu wata matsala a Kwankwasiyya domin shugaban ta, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso mutum ne mai adalci, inda ya kara da cewa duk wata fitina da za ta taso wa kwankwaso da Kwankwasiyyar to a shirye ya ke da ya tare ta, da ƙirjinsa ma .

Sanata Shehu Sani yayi martani ga kalaman tsohon Kakakin Majalissar Kaduna Yusuf Zailani.Kayi dan majalissa shekara 20 k...
30/05/2026

Sanata Shehu Sani yayi martani ga kalaman tsohon Kakakin Majalissar Kaduna Yusuf Zailani.

Kayi dan majalissa shekara 20 kuma ka riqe Speaker amma sai nine na gina asibitoci 3 a Karamar Hukumar ka, a mazabar ka ma nagina asibiti nasaka kayan aiki, na dauki malamai ayau ana karbar haihuwa a wannan asibitoci.

Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya bukaci Gwamna Abba Kabir Yusuf da ya tabbatar da an yi amfani da ƙ...
29/05/2026

Mai Martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya bukaci Gwamna Abba Kabir Yusuf da ya tabbatar da an yi amfani da ƙarfin gwamnati wajen kare martaba da mutuncin gwamnati daga duk wanda ke ƙoƙarin ƙalubalantar ta.

Sarkin ya bayyana hakan ne yayin gudanar da Hawan Nasarawa a Fadar Gwamnatin Kano, inda ya kai ziyarar gaisuwar Sallah ga gwamnatin jihar Kano.

A jawabin nasa, Sarkin ya yaba da irin haɗin kai da goyon bayan da gwamnatin Kano ke bai wa masarautar, tare da jaddada cewa gwamnati tana da ikon kare kanta da kuma tabbatar da doka da oda a jihar.

Cika shekara uku a mulki: Tinubu ya ce sauye-sauyen tattalin arziki sun fara haifar da ɗa mai ido Shugaban Ƙasa Bola Ahm...
29/05/2026

Cika shekara uku a mulki: Tinubu ya ce sauye-sauyen tattalin arziki sun fara haifar da ɗa mai ido

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa Nijeriya ta fara fita daga mawuyacin halin rashin tabbas a fannin tattalin arziki, ya ce ƙasar tana kan turbar farfaɗowa da bunƙasa yayin da gwamnatin sa ta cika shekara uku a mulki.

A jawabin da ya yi ga al’ummar ƙasa domin bikin cika shekaru uku na mulkin sa a ranar wannan Juma'ar, Shugaba Tinubu ya amince cewa ‘yan Nijeriya sun sha wahalhalu sakamakon manyan sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin sa ta aiwatar, ciki har da cire tallafin man fetur da kuma haɗa tsarin canjin kuɗaɗen ƙasashen waje. Sai dai ya jaddada cewa waɗannan matakai sun zama dole domin kauce wa faɗuwar tattalin arziki da kuma shimfiɗa tubalin cigaba mai ɗorewa.

Shugaban ya ce lokacin da gwamnatin sa ta hau mulki a shekarar 2023, ƙasar nan tana fama da matsaloli masu yawa da s**a haɗa da matsin tattalin arziki, raguwar kuɗaɗen shiga, matsalolin tsarin canjin kuɗaɗen waje, hauhawar kuɗin biyan basuss**a, rashin tsaro da kuma raguwar amincewar jama’a da hukumomin gwamnati.

A cewar sa, Nijeriya na kashe kusan Naira biliyan 18.4 a kowace rana wajen tallafin man fetur, lamarin da ya kai sama da Naira tiriliyan 4 a shekarar 2022 kaɗai. Ya kuma ce tsarin canjin kuɗaɗen waje da yawa ya haifar da asarar sama da Naira tiriliyan 8 cikin shekaru uku sakamakon amfani da guraben da tsarin ya samar domin cin riba ba tare da samar da wata ƙima ga tattalin arziki ba.

“Zaɓi mafi sauƙi zai kasance mai amfani a siyasance, to amma shugabanci yana buƙatar jajircewa da ɗaukar matakan da s**a dace ko da kuwa suna da wahala,” inji Tinubu, yana mai cewa rashin ɗaukar waɗannan matakai zai iya jefa ƙasar nan cikin matsananciyar matsalar tattalin arziki da ƙarin talauci.

Da yake zayyana nasarorin da gwamnatin sa ta samu cikin shekaru uku, Shugaban ya ce tattalin arzikin Nijeriya ya zama mafi ƙarfi kuma ya fi dacewa da cigaba mai ɗorewa. Ya ce an samu ƙaruwar amincewar masu zuba jari, inganta kuɗaɗen gwamnati da kuma bunƙasar kasuwar hannayen jari, inda darajar kasuwar ta tashi daga Naira tiriliyan 30 a shekarar 2023 zuwa Naira tiriliyan 160 a shekarar 2026.

Tinubu ya kuma bayyana cewa ana gudanar da manyan ayyukan more rayuwa a faɗin ƙasar nan, inda ya ce fiye da kilomita 2,700 na manyan hanyoyi ake cikin ginawa, gyarawa ko faɗaɗawa. Ya ambaci Babban Titin Bakin Teku na Legas zuwa Kalaba, Babban Titin Sakkwato zuwa Badagiri, hanyar Abuja-Kaduna-Zariya-Kano da kuma titin Gabas zuwa Yamma a matsayin wasu daga cikin manyan ayyukan da ake aiwatarwa.

Ya ƙara da nuni da cewa ana ci gaba da aikin sabunta hanyoyin jirgin ƙasa domin inganta sufuri da haɗa yankunan ƙasar nan ta fuskar tattalin arziki.

A fannin mai da iskar gas, Shugaban ya ce sauye-sauyen da gwamnatin sa ta aiwatar sun jawo sababbin jarin biliyoyin daloli daga kamfanonin ƙasa da ƙasa. Ya kuma ce ƙarfin tace mai a cikin gida ya ƙaru, abin da ke rage dogaro da shigo da man fetur daga ƙasashen waje tare da adana kuɗaɗen musayar waje.

Game da wutar lantarki, Tinubu ya ce gwamnatin sa tana saka hannun jari wajen faɗaɗa hanyoyin isar da wuta, inganta tsarin sadarwa da kuma amfani da makamashi mai sabuntawa domin tabbatar da cewa tattalin arzikin ƙasar nan ya samu ingantaccen tushen cigaba.

Shugaban ya kuma bayyana nasarorin da aka samu a fannoni daban-daban kamar noma, ilimi, gidaje, lafiya, sadarwa da fasahar zamani. Ya ce shirye-shiryen tallafa wa manoma sun amfani miliyoyin manoma a faɗin ƙasar nan, yayin da Asusun Lamunin Ilimi na Nijeriya ya taimaka wa sama da ɗalibai miliyan 1.5 samun damar cigaba da karatu ta hanyar bayar da sama da Naira biliyan 282.

A ɓangaren gidaje kuwa, ya ce sama da gidaje 10,000 ne ake ginawa a jihohi 14 da Babban Birnin Tarayya ƙarƙashin Shirin 'Gidajen Renewed Hope' da na Hukumar Gidaje ta Tarayya, lamarin da ya samar da fiye da ayyukan yi 300,000.

Dangane da tsaro, Shugaban ya ce jami’an tsaro sun ƙara ƙaimi wajen yaƙi da ‘yan ta’adda, ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane, ɓarayin man fetur da sauran masu aikata laifuffuka. Duk da cewa har yanzu akwai ƙalubale, ya ce yankuna da dama da hanyoyi sun fi samun zaman lafiya fiye da da.

“Ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba har sai kowane ɗan Nijeriya ya samu damar rayuwa, aiki, tafiye-tafiye da cimma burin sa cikin tsaro,” inji shi.

Tinubu ya yi kira ga jama'ar ƙasa da su ci gaba da haɗin kai tare da kauce wa rarrabuwar kawuna, yana mai jaddada cewa cigaban Nijeriya yana buƙatar haɗin gwiwar kowa ba tare da la’akari da bambance-bambancen addini, yanki ko ƙabila ba.

“Dole ne mu zaɓi fata maimakon yanke ƙauna, haɗin kai maimakon rarrabuwar kawuna, da gina ƙasa maimakon son rai,” inji Shugaban.

Da yake duban gaba, Tinubu ya yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin rage farashin abinci da sufuri, samar da ƙarin ayyukan yi da kuma tabbatar da cewa amfanin sauye-sauyen tattalin arziki ya kai ga talakawan Nijeriya.

Ya sha alwashin cewa Nijeriya za ta fito daga ƙalubalen da take fuskanta cikin ƙarfi da wadata, yana mai cewa ƙasar tana fuskantar wani gwaji ne na tarihi wanda daga ƙarshe zai haifar da zaman lafiya, cigaba da haɗin kai.

“A yau duniya na sake kallon ƙasar mu, ba a matsayin ƙasar da matsaloli s**a bayyana ba, amma a matsayin ƙasar da ta ƙudiri aniyar tashi tsaye da cimma nasara,” inji shi.

Gyaran Tattalin Arziƙi na Tinubu: Nasarori da ƘalubaleGwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta aiwatar da sauye-sauye a ta...
29/05/2026

Gyaran Tattalin Arziƙi na Tinubu: Nasarori da Ƙalubale

Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta aiwatar da sauye-sauye a tattalin arziƙi da harkokin kuɗaɗe, ciki har da cire tallafin mai da daidaita tsarin canjin kuɗi.

Yayin da gwamnati ke cewa matakan sun taimaka wajen farfaɗo da tattalin arziƙi, ƴan ƙasa na ci gaba da kokawa kan tsadar rayuwa da hauhawar farashi.

Masana na ganin an samu wasu nasarori, amma har yanzu akwai ƙalubale da manufofin da ba a cimma ba musamman wajen rage talauci da samar da ayyukan yi.

Ya abin ya ke a wajenku?

Kwamared Aminu Abdussalam ya zama ɗan takarar gwamnan Kano na jam’iyyar NDC yayin da Gawuna ya amince da tikitin SanataK...
29/05/2026

Kwamared Aminu Abdussalam ya zama ɗan takarar gwamnan Kano na jam’iyyar NDC yayin da Gawuna ya amince da tikitin Sanata

Kwamared Aminu Abdussalam, tsohon mataimakin gwamnan Kano, ya zama ɗan takarar gwamna na jam’iyyar NDC a Jihar Kano bayan babban mai neman takarar kujerar, Nasiru Gawuna, ya amince da karɓar tikitin takarar Sanatan Kano ta Tsakiya.

📸Yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal, sun isa Budapest, inda zaa fafata wasan karshe na gasar kofin zakarun nahiy...
28/05/2026

📸Yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal, sun isa Budapest, inda zaa fafata wasan karshe na gasar kofin zakarun nahiyar Turai Champions League. ✅🇭🇺

Ana cigaba da samun turjiya a bangaren Kwankwasiyya kan zaben wanda zai yiwa Jam'iyyar Kano takara a karkashin Inuwar Ja...
28/05/2026

Ana cigaba da samun turjiya a bangaren Kwankwasiyya kan zaben wanda zai yiwa Jam'iyyar Kano takara a karkashin Inuwar Jam'iyyar NDC, tsakanin Comrade Aminu Abdulsalam da Nasiru Yusuf Gawuna.

Address


Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when A M T Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Organization

Send a message to A M T Hausa:

  • Want your organization to be the top-listed Government Service?

Share