Halacci Movement PDP Jigawa

Halacci Movement PDP Jigawa Labarai daga Jigawa

Ko mutum makaho ne yasan Mustapha Sule Lamido Better than Ɗan moɗi sau dubu wallahi ☝Ranar biyar aka haifeshiA watan biy...
23/08/2026

Ko mutum makaho ne yasan Mustapha Sule Lamido Better than Ɗan moɗi sau dubu wallahi ☝

Ranar biyar aka haifeshi
A watan biyar aka haifeshi
Shine Na Biyar a gidansu
munyi fatan ya zama gwabnan farar hula na biyar

Akwai shikimar ubangiji cikin wannan lamarin haqiqa Gobe Ta Alla Ce

mai Digiri uku akan Ilimin kimiyar siyasa(Political Science)

ya shugabancin Rukunin kamfanoni har guda uku

yayi dagaci tsawon shekara 8

yayi Sarautar Hakimi tsawon Shekara 10 yana da kwarewa(experience) akan sha'anin gudanar da Mulki

JAHUN TA ƊINKE 📌Tsohon Kakakin Majalisar dokokin Jihar Jigawa, Ɗan Majalisar Jiha mai wakiltar Jahun a zauren majalisar ...
19/08/2026

JAHUN TA ƊINKE 📌

Tsohon Kakakin Majalisar dokokin Jihar Jigawa, Ɗan Majalisar Jiha mai wakiltar Jahun a zauren majalisar dokokin Jihar Rt. Hon. Idris Garba Kareka, ya bar Jam'iyyar APC, ya shiga Jam'iyyar PDP.

Ana saran zai zama dan takarar majalisar tarayya a zaɓen 2027 domin wakiltar Kananan hukumomin Jahun da Miga gobe a Jahun da yardar Allah.

In za'a iya tunawa dama bai sabunta katinsa na zama dan Jam'iyyar APC ba a lokacin da aka yi, sannan tuni ya yi rijista da Jam'iyyar PDP kafin a rufe rijistar Jam'iyyu.

PDP POWER✅

DA DUMI-DUMI: Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da hukuncin da ya hana INEC amincewa da zaɓen shugabancin ADC na jihohiKotu...
13/07/2026

DA DUMI-DUMI: Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da hukuncin da ya hana INEC amincewa da zaɓen shugabancin ADC na jihohi

Kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja ta tabbatar da hukuncin da ya hana hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) amincewa ko shiga cikin tarukan zaɓen shugabannin jihohi na jam'iyyar ADC da ɓangaren da Sanata David Mark ke jagoranta ya gudanar.

Kotun ta yanke hukuncin ne a ranar Litinin, inda alkalai biyu s**a goyi bayan tabbatar da hukuncin, yayin da alƙali ɗaya ya nuna rashin amincewa.

Hakan ya tabbatar da hukuncin da mai Shari'a Joyce Abdulmalik ta babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke a ranar 29 ga Afrilu, 2026.

Da wannan hukunci, INEC za ta ci gaba da kasancewa ƙarƙashin umarnin kotu na rashin amincewa da tarukan zaɓen shugabannin jihohin da ɓangaren David Mark na jam'iyyar ADC ya gudanar, har sai an samu wani sabon hukunci daga kotu.

Ana sa ran za a fitar da cikakkun bayanan hukuncin nan gaba.

Jam'iyyar PDP ta Kasa ta bawa dan takarar Gwamnan Jigawa na Jam'iyyar Alhaji Mustapha Sule Lamido (Santurakin Dutse) sha...
24/06/2026

Jam'iyyar PDP ta Kasa ta bawa dan takarar Gwamnan Jigawa na Jam'iyyar Alhaji Mustapha Sule Lamido (Santurakin Dutse) shaidar lashe zaɓen cikin gida da kuma amincewar hukumar zabe ta Kasa na takararsa.

Shugaban Jam'iyyar PDP na Kasa Alhaji Abdulrahman Mohammed ne ya mika masa takardar yayin gudanar da taron tattaunawa na masu ruwa da tsakin Jam'iyyar na Kasa.

Allah yasa albarka
Allah ka iya mana
Allah ka yi mana Jagora.

YANZU-YANZU: Jam'iyyar PDP ta tsaida Professor Isa Ali Pantami CON a matsayin ɗan takarar Gwamnan jihar Gombe a zaɓe mai...
26/05/2026

YANZU-YANZU: Jam'iyyar PDP ta tsaida Professor Isa Ali Pantami CON a matsayin ɗan takarar Gwamnan jihar Gombe a zaɓe mai zuwa.

Jam’iyyar PDP a Jihar Jigawa ta bayyana shirinta na gudanar da taron tabbatar da Alhaji Mustapha Sule Lamido, wanda aka ...
23/05/2026

Jam’iyyar PDP a Jihar Jigawa ta bayyana shirinta na gudanar da taron tabbatar da Alhaji Mustapha Sule Lamido, wanda aka fi sani da Santurakin Dutse, a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.

An shirya gudanar da taron ne ranar Lahadi 24 ga watan Mayun 2026 da ƙarfe 10:00 na safe a dakin taro na MTown Hotel, kusa da Aminu Kano Triangle da ke kan titin Kiyawa a birnin Dutse.

Mustapha Sule Lamido, ɗan tsohon gwamnan Jihar Jigawa Alhaji Sule Lamido, shi ne ya wakilci PDP a zaɓen gwamna na 2023, kuma a baya-bayan nan ya samu goyon baya daga wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar da masu ruwa da tsaki a jihar.

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, , ya yi kira na musamman ga tsohon shugaban ƙasar Najeriya, , da ya dakatar da duk wani yun...
20/05/2026

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, , ya yi kira na musamman ga tsohon shugaban ƙasar Najeriya, , da ya dakatar da duk wani yunƙuri na komawa cikin siyasar Najeriya a wannan lokaci da ƙasar ke fuskantar yanayin siyasa mai cike da ruɗani.

Lamido ya bayyana cewa Jonathan ya fahimci matsayinsa a Najeriya a matsayin jagora kuma tsohon shugaban ƙasa, wanda hakan ya sanya ya zama wata alama ta haɗin kan ƙasa. Ya ƙara da cewa Jonathan na cikin jerin manyan shugabannin duniya da ake girmamawa a matakin ƙasa da ƙasa.

A cewarsa, bai dace a jawo Jonathan cikin wannan yanayin siyasa mai cike da son kai da neman anfani na kashin kai ba, musamman ganin cewa saura kwanaki kaɗan a rufe tantancewar ‘yan takarar da za su fafata a zaɓen shekarar 2027.

Lamido ya ce jam’iyyun siyasar Najeriya sun rarrabu tare da rasa cikakkiyar manufa ta siyasa, inda mafi yawansu s**a mayar da hankali kan neman mulki kawai.

Ya bayyana cewa kiraye-kirayen da ake yi wa Jonathan ya dawo siyasa — ko da kuwa da kyakkyawar niyya ake yi — sun samo asali ne daga halin rashin tabbas da takaicin da Najeriya ke ciki.

“A halin yanzu, Jonathan ya kamata ya ci gaba da riƙe matsayinsa na mutunci da kima a matsayin wani ginshiƙi na ƙasa baki ɗaya,” in ji Lamido.

Ya ƙara da cewa duk da ana yaba irin wannan kira, amma kira ne na gaggawa da takaici wanda bai wuce bayyana damuwar jama’a ba.

Lamido ya jaddada cewa Jonathan bai kamata ya bari irin wannan kira na lallashi ya jawo shi komawa siyasa yanzu ba, yana mai cewa har yanzu akwai damar a ajiye shi domin wani lokaci na gaba.

CANJIN SHEKA DAGA APC ZUWA PDPTsohon ɗan majalisar jiha mai wakiltar Gwaram ta Arewa, Tsohon Kakakin Majalisar Dokokin J...
06/05/2026

CANJIN SHEKA DAGA APC ZUWA PDP

Tsohon ɗan majalisar jiha mai wakiltar Gwaram ta Arewa, Tsohon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Jigawa, Tsohon mataimakin Shugaban karamar hukumar Gwaram, Tsohon SSA kan harkokin Hajji, Alh. Hon Isha Idris Gwaram (Jagora) ya fice daga APC tare da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar PDP.

DA DUMI-DUMI: Bangaren PDP ƙarƙashin jagorancin Turaki ya sha kaye, yayin da Kotun Ƙoli ta soke taron Ibadan.Kotun ta ku...
30/04/2026

DA DUMI-DUMI: Bangaren PDP ƙarƙashin jagorancin Turaki ya sha kaye, yayin da Kotun Ƙoli ta soke taron Ibadan.

Kotun ta kuma amince da shugabancin jam’iyyar na ɓangaren da Wike ke mara wa baya, inda tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya shigar da kara tun farko.

Address

Jigawa
Jigawa

Telephone

+2348032820280

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Halacci Movement PDP Jigawa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share