04/06/2026
Inna lillahi wa inna ilayhi raji’un.
Hakika na jima banga abin da ya tayar min da hankali kamar Wannan video din ba. Na kasa samun natsuwa tun lokacin da na kalli wannan video na wasu dattawa daga Karamar Hukumar Mulki ta Koko Besse, Kebbi State da ke hannun masu garkuwa da mutane.
Babu shakka duk wani mai imani da tausayin bil’adama, idan ya kalli wannan video din, dole ne zuciyarsa ta ji zafi da tausayi. Bayan wulakanci da rashin mutunci da wayannan yaran masu garkuwa da mutane su ke musu, waɗanda ba su wuce warin jikokin su ba kuma s**a tubesu suna ɗaukar su video acikin daji, gasu daure suna azabtar da su duk da halin rashin lafiyarsu.
Tun da na kalli wannan bidiyo, zuciyata tana ciwo da fushi da damuwa. Ina ta tunanin cewa idan wannan hali ya ci gaba, kuma shugabanninmu suna kwanciya suna bacci cikin natsuwa, to da gaske ba su cancanci mulkin ko da Dabbobi ba, ballantana ku ma Mutane bil adama.
Abin takaici ne cewa duk wannan halin da ake ciki a ƙasar nan, musamman a Arewacin Najeriya, wasu mutane a shafukan sada zumunta suna shagaltuwa da zagi da rigingimu kan batutuwan siyasa da s**a shafi tarihin kisan Sardauna na Sokoto da Sir Abubakar Tafawa Balewa, da kuma magoya bayan Peter Obi da Kwankwaso. A irin wannan lokaci, ya kamata mu mayar da hankali wajen haɗin kai da kira ga gwamnati ta ɗauki mataki mai ƙarfi wajen kawo ƙarshen wannan matsala, ko kuma a canja ta idan lokaci ya yi. Amma sai muka mayar da hankali kan abin da ba zai amfane mu ba face rarrabuwar kawuna da koma baya.
Ina roƙon Allah Ya tayar da ‘yan Arewa su farka daga barci su san irin bala'in daya tunkaro su domin lallabo hanyar magangace mala'in da kuma tarin Matsalolin dake faruwa a kasar nan.
Ya Allah, Ubangijin sammai da ƙasa, Ka hallaka duk wanda ke da hannu a tashin hankalin ƙasarmu Nigeria. Idan wandake da mulki ne a cikinsu Ka amshe mulkin nasa, idan kuma mai sarauta ne Ka cire shi daga sarauta; idan kuma ma’aikaci ne Ka sauke shi daga mukaminsa; idan kuma ɗan kasuwa ne mai tallafa musu Ka tauye arzikinsa; idan kuma talaka ne mai taimaka musu Ka tona asirinsu ka wulakanta su a duniya kafin lahira. Idan sun mutu a haka basu tubaba, Ya Allah Ka saka su a azabar da ta dace da su.
Ya Allah Ka kawo ƙarshen wannan tashin hankali, Ka kawo mana zaman lafiya a ƙasarmu. Amin.
Sabar International Community Foundation (SICFO)