18/01/2026
Runner ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta sanar da k**a mutane uku da ake zargi da hannu a kisan gillar da aka aikata a ranar 17 ga Janairu, 2026, a unguwa Dorayi Chiranchi, sak**akon umarnin da Inspector-General Kayode Adeolu Egbetokun ya bayar.
A cewar rundunar, Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya jagoranci wani rukuni na musamman da ya gudanar da samame daga karfe 10 na dare zuwa 4 na asuba, inda aka k**a Umar Auwalu (23), Isyaku Yakubu (40) da Yakubu Abdulaziz (21).
Rundunar ta bayyana cewa Umar Auwalu, wanda ake zargi shi ne shugaban ƙungiyar, kuma ɗan’uwan wadda aka kashe, ya amince da aikata kisan. Haka kuma, ya amince da aikata wasu laifukan tashin hankali a baya, ciki har da kisan mutane biyu a Tudun Yola.
An ce shaidun da aka samu a wajen sun haɗa da tufafin da jini ya jika, wayoyin salula na wadda aka kashe, da mak**ai daban-daban. Rundunar ‘yan sanda ta gode wa al’umma kan bayar da haɗin kai, tare da jaddada cewa bincike na ci gaba.