14/04/2026
๐๐ฐ๐๐ฆ๐ง๐๐ง ๐๐ข๐ก๐๐ซ ๐๐๐ญ๐ฌ๐ข๐ง๐ ๐๐ซ. ๐๐ข๐ค๐ค๐จ ๐๐ฆ๐๐ซ ๐๐๐๐๐ ๐๐ก๐ ๐๐๐๐ Duk Wanda Aka K**a Yazo Karษar Belin ฦauraye To Shi ma Zaโa Yanke Masa Hukunci Irin Na ฦaurayeโ
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, PhD, ya bayyana hakan ne yayin da yake sanya hannu kan wata Doka ta musamman da ke da nufin dakile matsalar Kauraye da sauran masu aikata laifuka a faษin jihar.
An sanya wa dokar, mai taken Katsina State Kauraye Activities and Operations Order 2026, hannu a Gidan Gwamnati da ke Katsina, a gaban manyan jamiโan tsaro da hukumomin gwamnati da abin ya shafa.
Gwamna Radda ya bayyana cewa an ษauki wannan mataki ne sak**akon ฦaruwa da ake samu na ayyukan da s**a saษa wa doka, musamman a cikin birnin Katsina. Ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta zura ido ta bari rashin tsaro da aikata laifuka su ci gaba ba. Ya kuma ce kare rayuka da dukiyoyin alโumma na daga cikin manyan abubuwan da gwamnatinsa ta sa a gaba.
A matsayin wani ษangare na sabbin matakan, Gwamnan ya amince da kafa Kwamiti na Musamman na Aiki wanda ya ฦunshi jamiโan Rundunar โYan Sandan Najeriya, DSS, NSCDC, NDLEA, Community Watch Corps, Hukumar Hisbah, Maโaikatar Tsaron Cikin Gida da Harkokin Cikin Gida, Maโaikatar Shariโa, Maโaikatar ฦananan Hukumomi da Harkokin Masarautu, da kuma ALGON.
An ษora wa kwamitin alhakin gano da rushe ฦungiyoyin masu aikata laifi, gudanar da ayyukan sirri na tsaro, k**a waษanda ake zargi, ฦwace mak**ai da sauran kayayyakin da ake amfani da su wajen aikata laifi, sa ido kan wuraren da ake yawan aikata laifi, da tabbatar da gurfanar da masu laifi a gaban kuliyar tafi da gidanka. Haka kuma zai yi aiki tare da shugabannin alโumma, sarakuna, da malamai domin hana ษaukar matasa cikin irin waษannan ฦungiyoyi.
Gwamna Radda ya kuma sanar da kafa Kotun Tafi-da-Gidanka domin tabbatar da gaggauta shariโar masu laifi. Sannan ya sanar da cewa duk wanda yazo neman belin wadanda aka k**a da wannan laifuka to shima doka zata ษauki mataki kanshi. Wannan shiri zai gudana ne haษin gwiwa tsakanin Maโaikatar Shariโa da Ofishin Babban Alฦalin Jihar Katsina.
Ya ฦara da cewa wannan Dokar na daga cikin manyan matakan da gwamnatinsa ke ษauka domin dawo da zaman lafiya, ฦarfafa tsaron cikin gida, da samar da ingantaccen yanayi ga dukkan alโummar Jihar Katsina.
Wadanda s**a halarci taron sun hada da sakataren gwamnati, Barr. Abdullahi Garba Faskari, PPP, Alh Abdullahi Aliyu Turaji, Kwamishinan Harkokin Tsaro, Kwamishinan Harkokin Shariโah, Shugaban Karamar Hukumar Katsina, Hon Isah Miqdad, Wakilin Kwamishinan Yan Sanda da sauransu.
MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government
April 14, 2026.