08/08/2026
Gwamna Malam Umar Namadi a yau ya halarci bikin ɗaura auren ma'aurata 1,500 da Gwamnatin Jihar Kano ta ɗauki nauyi ta hannun Hukumar Hisbah ta Jihar Kano. An gudanar da bikin ne a harabar Gidan Gwamnatin Jihar Kano.
Bikin ya samu halartar manyan baƙi da s**a haɗa da Gwamnan Jihar Katsina, Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi, manyan malaman addinin Musulunci (Ulama) da sauran manyan baki.
Gwamna Namadi ya samu rakiyar Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Jigawa, Rt. Hon. Haruna Aliyu Dangyatin, zuwa wajen bikin.