06/05/2026
KUNGIYAR MATASA YAN GWARAM MAZAUNA BAUCHI
TAKARDAR JAJANTAWA DA KUMA KARFAFA GWIWA GA ALH. ADAMU YUSUF GARKUWAR DUTSE.
Assalamualaik*m warahmatullahi wabarakatuhu,
Muna farawa da godiya wa Allah (s.w.t) bisa ni'imomi da yayi mana wadanda baza mu iya Lissafasuba cikin su harda Imani da kaddara mai kyau da Kuma maras kyau, Allah ta'ala yasa mugama da duniya lafiya.
Bayan haka Muna Fatan alkairi tare da dukkan girmamawa agareka jinjina da addu'o'i agareka Allah ya kara Maka lafiya, Imani, nisan kwana mai albarka, kyautatawa mutane, taimakon al'umma tare da arziki mai yawa mai albarka.
Muna Mika sakon jaje bisa wannan qaddara ta jarrabawa da Allah ya hukunta agareka da mu gabaki daya, Muna sake baka hakuri, lallashi cikin alhini da taushin zuciya, Allah ta'ala ya sa wannan al'amari yazama silar sabuwar daukaka da dubban alkairan dama bamusan da suba.
Akarshe Muna kara Maka kwarin gwiwa da kara Maka goyon baya da Kuma kira da kada a gajiya Kuma kada a hakura acigaba da gogwararmaya domin akwai haske sosai awannan tafiyar, domi babu wani mai neman kujera a jigawa bama a Gwaram ba dayayi farin jini da samun goyon baya a cikin al'ummar sa kamar ka Don haka muna kara rokonka da ka cigaba da wannan gwagwarmaya har Allah ta'ala ya sa mukai ga nasara.
Jinjina da fatan nasara.
KUNGIYAR MATASA YAN GWARAM MAZAUNA BAUCHI
06/05/2026.
19/11/1447AH