30/03/2026
Wani matashin dan siyasa a jihar Bauchi, Nasiru Chigari, ya mayar da martani ga masu s**ar tsohuwar Kwamishinar Harkokin Mata da ci gaban kananan yara ta jihar, Hajiya Zainab Babantakko, kan matakin da ta dauka na ficewa daga jam’iyyar PDP.
A cikin wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Chigari ya bayyana cewa tun bayan da aka sauke Babantakko daga mukaminta, ba a taba jin ta furta wata kalma da za ta zubar da mutuncin Gwamnan jihar Bauchi ko gwamnatinsa ba.
Ya ce duk da rade-radin zarge-zargen da aka yi mata, wanda ake zargin shi ya kai ga sauketa daga kujerar kwamishina, har yanzu akwai tambayoyi da dama da ke tattare da zarge-zargen, yana mai cewa ba a tabbatar da su ba.
Chigari ya kara da cewa, bayan dawowarta daga hutun da ta yi a kasashen ketare, Babantakko ta sake jaddada godiyarta ga gwamnan bisa damar da ya bata tare da yi masa fatan alheri.
A cewarsa, “tarihi bai nuna cewa ana bai wa mutum mukamin siyasa ba tare da la’akari da gudunmawar da ya bayar ba, domin kusan kashi 99 cikin 100 na mukamai ana bayar da su ne bisa irin gudunmawar da aka bayar a lokacin neman zabe.”
Ya kuma bayyana cewa su a matsayin ‘yan asalin karamar hukumar Bauchi kuma ‘yan jam’iyyar PDP, sun san irin rawar da Babantakko ta taka wajen ganin jam’iyyar ta samu nasara, musamman a zaben shekarar 2023.
Dangane da ficewarta daga jam’iyyar PDP kuwa, Chigari ya ce bai kamata a dauki hakan a matsayin laifi ba, yana mai cewa, “a wannan lokaci da kowa ke neman mafita ga rayuwarsa ta siyasa, ba za a zargi Zainab Babantakko ba saboda kawai ta bi sahun dubban ‘yan siyasa wajen neman mafitarta.”
Ya kuma yi nuni da cewa kafin ta bayyana matsayarta, wasu daga cikin makusantan gwamnan ciki harda 'ya'yansa sun riga sun dauki irin wannan mataki a aikace, don haka bai dace a yi mata kallon daban ba.
A karshe, Chigari ya yi kira ga masu s**ar ta da su yi adalci a ra’ayoyinsu, yana mai jaddada cewa lamarin Babantakko ya shafi al’umma gaba daya, ba wai bangaren jam’iyya ko yanki kadai ba.